Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
Published: 15th, March 2025 GMT
A jiya juma’a ne dai firma ministan kasar Iraki Muhammad Shi’ya al-Sudani ya sanar da cewa sojojin kasar sun kashe babban dan ta’adda Abdullahi Makki wanda ake yi wa lakabi da Abu Hadiza.
Al-Sudani ya kara da cewa; Iraki taba cigaba da samun nasara akan ‘yan ta’adda, bayan da jami’an tsaro na kasa da kasa su ka yi nasarar kashe Abdullahi al-makki, wanda ya kasance a matsayin mataimakin shugaban abind ake kira da Daular Musulunci a Iraki da Syria.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
Dakarun Sojin Operation Whirl Stroke (OPWS), sun kashe wasu mutum uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, yayin wani samame da suka kai a Ƙaramar Hukumar Ukum, a Jihar Binuwai.
Mai magana da yawun OPWS, Laftanar Ahmad Zubairu, ya ce sojojin sun samu bayanan sirri kuma suka yi aiki tare da ’yan sandan Zaki-Biam.
Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a KatsinaMaharan sun kafa shinge a kan hanyar Aturuku–Wembe–Ayati, inda suke tare matafiya suna ƙwace musu kayayyaki.
Da sojoji suka isa wajen, maharan sai suka fara harbe-harbe, wanda hakan ya sa sojojin suka buɗe musu wuta.
Hakan ya yi sanadin mutuwar uku daga cikinsu, sauran kuma suka tsere cikin daji.
Dakarun sun ƙwato babura guda biyu, yayin da suka ci gaba da farautar waɗanda suka tsere.
Bincike ya nuna cewa mutanen da suka mutu suna cikin wata ƙungiya da ta daɗe tana yi wa al’umma barazana ta hanyar garkuwa da mutane da kai hare-hare, musamman kusa da kasuwar doyar Zaki-Biam.
Mutanen gari sun tabbatar da sunan waɗanda dakarun suka kashe.
Kwamandan OPWS, Manjo-Janar Moses Gara, ya yaba wa sojojin bisa ƙwazo da jarumtarsu, tare da alƙawarin ci gaba da kare al’umma da tabbatar da zaman lafiya.