Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha
Published: 12th, March 2025 GMT
Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta na wata guda a yaƙin da ta shafe shekaru uku tana fafatawa da kasar Rasha.
Matakin na zuwa ne bayan tattaunawar da wakilan ƙasar ke ci gaba da yi yanzu haka da Amurka a birnin Jedda na Saudiya.
Matashin da ke ƙera jiragen sama da bindigogi daga robobi Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a NasarawaSakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ne ya sanar da haka da maraicen Talata bayan shafe wuni guda jami’an Ukraine da na Amurka suna tattaunawa don samar da zaman lafiya tsakanin Ukraine din da Rasha.
Rubio ya ce makasudin gabatar da kudurin shi ne na dakatar da bude wuta da kashe mata da kuma kananan yara a Ukraine.
Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage ga Rasha na ta amince da kudurin ko kuma akasin hakan.
Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage wa Rasha, inda kowanne lokaci daga yanzu ne ake shirin miƙa mata ƙunshin matsayar da aka cimma a wannan taro na Jedda don nazartarta da kuma yiwuwar aminta da ita ko akasin haka.
Wasu majiyoyi sun bayyana yiwuwar Donald Trump ya tattauna da Vladimir Putin a cikin makon nan bayan matakin na Ukraine dangane da amincewa da tayin Washington kan tsagaita wuta a yaƙin ɓangarorin biyu.
Har ila yau, Amurkar ta kuma amince ta koma bai wa Ukraine din bayanan sirri da kuma tallafin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Petro: Man fetur shine burin Amurka a Venezuela ba yaki da fataucin kwayoyi ba
Yayin da ayyukan sojin Amurka ke karuwa a yankin Caribbean da Pasifik, shugaban kasar Colombia Gustavo Petro ya zargi gwamnatin Trump da yin amfani da matsin lamba kan kasar Venezuela da sunan yaki da fataucin muggan kwayoyi a matsayin hujjar samun damar shiga kasar don mamaye albarkatun man fetur da Allah ya huwace wa kasar.
Man fetur shine tushen al’amarin, Petro ya fadawa CNN a cikin wata hira ta musamman, yana mai cewa Venezuela ita ce kasar da tafi kowace kasa yawan danyen ma a duniya.
“Saboda haka, wannan batun baki dayansa a kan man fetur ne. Na yi imani cewa (Shugaban Amurka Donald Trump) na tunanin yadda zai samu mai a kasar Venezuela ne ba batun dimokiradiyya ko yaki da fataucin miyagun ƙwayoyi ba ne, “in ji shi.
Petro ya bayar da hujjar cewa man fetur na Venezuela ya kasance a sahun gaba game da manufofin Amurka. Ya bayyana cewa kadan ne kawai na cinikin magunguna a duniya ke bi ta kasar Venezuela kuma ba a daukar kasar a matsayin babbar mai samar da su.
A ranar Talata, Petro ya zargi Amurka da yunkurin dawo da wani sabon mulkin mallaka a kan kasashen latin.
Da yake mayar da martani, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka ya ce gwamnatin Trump za ta ci gaba da ayyukanta na yaki da muggan kwayoyi a yankin Caribbean da kuma jajircewarta na kare Amurkawa daga abin da ya kira mummunar gubar gwamnatin Maduro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tarayyar Afirka ta yi Allah wadai da juyin mulkin a Guinea-Bissau November 28, 2025 Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi November 27, 2025 Iran ta yi tir da Australiya kan alakanta IRGC, da mai tallafawa ta’addanci November 27, 2025 Ramaphosa ya soki Trump kan hana shi halartar taron G20 na badi November 27, 2025 ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau November 27, 2025 Faransa, Jamus, Italiya, da Burtaniya sun yi tir da “karuwar rikici” a yammacin kogon jodan November 27, 2025 Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci November 27, 2025 Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci