Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha
Published: 12th, March 2025 GMT
Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta na wata guda a yaƙin da ta shafe shekaru uku tana fafatawa da kasar Rasha.
Matakin na zuwa ne bayan tattaunawar da wakilan ƙasar ke ci gaba da yi yanzu haka da Amurka a birnin Jedda na Saudiya.
Matashin da ke ƙera jiragen sama da bindigogi daga robobi Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a NasarawaSakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ne ya sanar da haka da maraicen Talata bayan shafe wuni guda jami’an Ukraine da na Amurka suna tattaunawa don samar da zaman lafiya tsakanin Ukraine din da Rasha.
Rubio ya ce makasudin gabatar da kudurin shi ne na dakatar da bude wuta da kashe mata da kuma kananan yara a Ukraine.
Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage ga Rasha na ta amince da kudurin ko kuma akasin hakan.
Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage wa Rasha, inda kowanne lokaci daga yanzu ne ake shirin miƙa mata ƙunshin matsayar da aka cimma a wannan taro na Jedda don nazartarta da kuma yiwuwar aminta da ita ko akasin haka.
Wasu majiyoyi sun bayyana yiwuwar Donald Trump ya tattauna da Vladimir Putin a cikin makon nan bayan matakin na Ukraine dangane da amincewa da tayin Washington kan tsagaita wuta a yaƙin ɓangarorin biyu.
Har ila yau, Amurkar ta kuma amince ta koma bai wa Ukraine din bayanan sirri da kuma tallafin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
Matatar man Dangote ta sake rage farashin man fetur ɗin da take sayar da man, inda ta rage farashin man fetur ɗin daga Naira 828 zuwa Naira 699 kan kowace lita.
Bayanan farashin da aka wallafa a shafin kasuwancin farashin man fetur a Petroleumprice.ng a ranar Juma’a sun nuna cewa matatar ta aiwatar da wani bita na baya-bayan nan, inda ta rage farashin man da N129 a kowace lita – ragin kashi 15.58 cikin 100.
Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a KatsinaWani jami’in matatar man da ya zanta da manema labarai bisa sharaɗin sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin tsokaci a bainar jama’a, shi ma ya tabbatar da yin ragin.
Ya ce, matatar man ta rage farashin man fetur zuwa N699 kowace lita.
Sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 11 ga watan Disamba, 2025, wanda ya yi daidai da farashin man fetur karo na 20 da matatar man ta sanar a bana.
Ragi na baya-bayan nan ya zo ne kwanaki biyar bayan shugaban matatar, Aliko Dangote ya jaddada ƙudirinsa na ganin an tabbatar da farashin man fetur a cikin gida cikin “madaidaicin farashi a kasuwanni” duk kuwa da taɓarɓarewar da ake samu a duniya da fasaƙwaurin da ake yi a kan iyakokin Najeriya.
Da yake bayani bayan ganawar sirri da shugaban Najeriya, Bola Tinubu a ranar 6 ga watan Disamba, Dangote ya ce farashin zai ci gaba da faɗuwa yayin da matatar man ke ƙara yawan kayan da ake fitarwa da kuma yin gogayya kai tsaye da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje.