Aminiya:
2025-12-10@21:35:52 GMT

Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha

Published: 12th, March 2025 GMT

Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta na wata guda a yaƙin da ta shafe shekaru uku tana fafatawa da kasar Rasha.

Matakin na zuwa ne bayan tattaunawar da wakilan ƙasar ke ci gaba da yi yanzu haka da Amurka a birnin Jedda na Saudiya.

Matashin da ke ƙera jiragen sama da bindigogi daga robobi Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ne ya sanar da haka da maraicen Talata bayan shafe wuni guda jami’an Ukraine da na Amurka suna tattaunawa don samar da zaman lafiya tsakanin Ukraine din da Rasha.

Rubio ya ce makasudin gabatar da kudurin shi ne na dakatar da bude wuta da kashe mata da kuma kananan yara a Ukraine.

Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage ga Rasha na ta amince da kudurin ko kuma akasin hakan.

Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage wa Rasha, inda kowanne lokaci daga yanzu ne ake shirin miƙa mata ƙunshin matsayar da aka cimma a wannan taro na Jedda don nazartarta da kuma yiwuwar aminta da ita ko akasin haka.

Wasu majiyoyi sun bayyana yiwuwar Donald Trump ya tattauna da Vladimir Putin a cikin makon nan bayan matakin na Ukraine dangane da amincewa da tayin Washington kan tsagaita wuta a yaƙin ɓangarorin biyu.

Har ila yau, Amurkar ta kuma amince ta koma bai wa Ukraine din bayanan sirri da kuma tallafin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin barkina faso ta sanar da sakin jami’an sojin saman nigeriya guda 11 da suka yi saukar gaggawa da jirginsu mai lamba C-130 a birnin Ouagadugu da ta bayyana saukar ta su ta gaggawa ce ba shiri, saboda matsala da jirgin ya samu a cewarsu,

Daga cikin Jami’an soji akwai matuka jirgi biyu sai fasinjoji guda 9 an kamasu domin gudanar da bincike saboda zargin da ake musu na cewa jirgin yana da alaka da juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar benin, kafin daga baya a sake su kuma tuni suka isa Najeriya.

A wani bayanin hadin guiwa da gwamnatocin soji na kasashen borkina faso da mali da Niger suka fitar karkashin lemar kungiyar Allience of sahel state sun bayyana abinda ya faru a matsayin keta hurumin sararin samaniyar kasar kuma ya sabama doka, sai dai sun ce lamarin ya sanya jamai’an sojin samansu cikin shirin ko ta kwana.

Najeriya ta ce jirgin ya yi saukar gaggawa ne saboda matsalar da ya samu, sai dai jami’an borkina faso sun yi zargin cewa jirgin ya shiga sararin samaniyarsu ba tare da izinin ba, kuma jami’ansu suna aiki da dokokin tashi da saukar jiragen sama don tsaron kasar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi December 10, 2025 Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu December 10, 2025 Najeriya: Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin December 10, 2025 Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama December 10, 2025 Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki December 10, 2025 Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  •  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  • Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta
  • Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma