Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]
Published: 10th, March 2025 GMT
Shehun malami al-Imam Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya bayyana cewa babban dalilin da ya sa Alƙur’ani ya sauka shi ne kira ga bautar Allah da shiga cikin addininsa. Wannan magana tana da tushen ilimi mai zurfi wanda ke da nasaba da tauhidi da shari’a, da hikimar shiriya.
1. Tauhidi a Matsayin Asalin Kiran Alƙur’ani: Manufar farko da Alƙur’ani ya zo da ita; ita ce tabbatar da tauhidi, wato bautar Allah Shi kaɗai ba tare da sanya masa abokin tarayyaba.
2. Shiga Cikin Addinin Allah: Manufar Alƙur’ani ta bautar Allah za ta samu ba sai a cikin addinsa. Don haka sai an shiga cikin addininsa da shari’ar da ya saukar, wato addinin Musulunci. Wannan yana nufin a bi dukan dokokin Allah da shari’o’in da suka zo a cikin Alƙur’ani da Sunnah. Allah Yana cewa: “Lalle addini a wurin Allah shi ne Musulunci.” Suratu Ãli Imrãn aya ta 19. Kuma ko mutum ya yarda da bautar Allah amma bai karɓi Musulunci ba, to Allah ba Zai karɓa masa ba, domin Ya ce:” Duk kuma wanda ya nemi bin wani addini ba Musulunci ba, to har abada ba za a karɓa daga gare shi ba, kuma shi a lahira yana cikin hasararru ” Suratu Ãli Imrãna aya ta 85. Wannan yana nuna cewa manufar Alƙur’ani ita ce shiryar da mutane su shiga cikin Musulunci ta hanyar yin imani da Allah da biyayya ga umarninsa.
3. Alƙur’ani A Matsayin Hujja: Saukar da Alƙur’ani yana ɗauke da cikakken tsarin rayuwa wanda yake jagorantar Musulumi a cikin dukan al’amuransu. Ya ƙunshi dokokin ibada kamar sallah da azumi da zakka da kuma hajji, da sauran su. Kuma ya ƙunshi dokokin mu’amala kamar ciniki da aure da kasuwanci, da sauran su. Hakanan Ya ƙunshi kyawawan ɗabi’u kamar gaskiya da zumunta, da , haƙuri da adalci da roƙon amana da sauran su. Kuma ya ƙunshi hukunce-hukunce da shari’a kamar halas da haram. Wannan yana nuna cewa saukar da Alƙur’ani ba wai kawai don sanin Allah ba ne, har ma don rayuwar duniya da lahira.
4. Manufar Saukar da Alƙur’ani ta Ķunshi dukan Halitta: Saukar da Alƙur’ani haske ne ga duniya baki ɗaya, mutane da aljanu, da ƙwari da dabbobi da halittu baki ɗaya, domin dukansu su san hanyar shiriya. Saboda haka, yana kira ga: da bin Alƙur’ani, kowa ya yi imani da Allah kaɗai ne abin bauta ba tare da an sanya masa kini ba. Mushrika da Ahlul Kitabi, wato Yahudu da Nasara da Maguzawa da kowa da kowa da su kaɗaita Allah da bauta, su shiga addininsa, kuma su bi shiriyarsa a kowane al’amari na rayuwarsu.
A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai tana bayani a kan cewa Alƙur’ani ya zo ne domin:
1. Kiran mutane su bauta wa Allah shi kaɗai,
2. Shiriyar da mutane zuwa ga addinin Musulunci,
3. Tabbatar da doka da tsarin rayuwa mai cike da adalci,
4. Fitar da mutane daga duhun jahilci zuwa hasken shiriya, domin samun jin daɗin duniya da lahira.
Wannan shi ne babban abin da Alƙur’ani ya zo da shi, kuma dukkan surori da ayoyinsa suna bayani ne akan waɗannan ginshiƙai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Alƙur ani ya bautar Allah
এছাড়াও পড়ুন:
Olisa Metuh ya sauya sheƙa zuwa APC, ya ce PDP ta manta da shi
Tsohon mai magana da yawun jam’iyyar PDP na ƙasa, Olisa Metuh, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Ya ce ya yanke wannan shawara ne saboda PDP ta kasa goyon bayansa lokacin da yake cikin matsaloli.
Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a SakkwatoMetuh, ya daina shiga harkokin siyasa kusan shekaru uku da suka wuce, ya amma ya dawo siyasa ne ta hanyar sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki.
Ya bayyana hakan ne a lokacin bikin cikarsa shekaru 60 a duniya, wanda ya gudana a Abuja.
Manyan ’yan siyasa da dama sun halarci taron, ciki har da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Anyim Pius Anyim, da tsoffin gwamnonin Abiya, Ebonyi da Imo.
Da yake magana da ’yan jarida bayan taron, Metuh, ya ce yana son ya taimaka wajen ci gaban Najeriya ta hanyar komawa APC.
Ya ce Najeriya na fuskantar ƙalubale, kuma yana son ya bayar da gudummawarsa a aikace.
Ya ce: “Lokacin da na shiga matsala, ban ga jam’iyyata ba. Na kasance a kotu tare da iyalina kawai.
“Amma Shugaba Tinubu, wanda nake suka a kai a kai, shi ne ya turo Femi Gbajabiamila ya zo ya duba ni ya kwantar min da hankali.”
Ya ce yana yi wa PDP fatan alheri, amma zai ci gaba da rayuwarsa ba tare da ita ba.
Haka kuma ya bayyana cewa har yanzu akwai jagorori masu ƙarfi a tsagin ’yan adawa, don haka Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya guda ɗaya ba.
Metuh, ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya sha yi masa tayin shiga APC, amma ya ƙi amincewa.
A cewarsa: “Shugaban ƙasa ya so na jam’iyyarsa tun 2015. Har bayan da na daina siyasa a 2022, ya sake gayyata ta, amma na ki. Yanzu da na koma siyasa, ina son na taimaka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya.”