Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]
Published: 10th, March 2025 GMT
Shehun malami al-Imam Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya bayyana cewa babban dalilin da ya sa Alƙur’ani ya sauka shi ne kira ga bautar Allah da shiga cikin addininsa. Wannan magana tana da tushen ilimi mai zurfi wanda ke da nasaba da tauhidi da shari’a, da hikimar shiriya.
1. Tauhidi a Matsayin Asalin Kiran Alƙur’ani: Manufar farko da Alƙur’ani ya zo da ita; ita ce tabbatar da tauhidi, wato bautar Allah Shi kaɗai ba tare da sanya masa abokin tarayyaba.
2. Shiga Cikin Addinin Allah: Manufar Alƙur’ani ta bautar Allah za ta samu ba sai a cikin addinsa. Don haka sai an shiga cikin addininsa da shari’ar da ya saukar, wato addinin Musulunci. Wannan yana nufin a bi dukan dokokin Allah da shari’o’in da suka zo a cikin Alƙur’ani da Sunnah. Allah Yana cewa: “Lalle addini a wurin Allah shi ne Musulunci.” Suratu Ãli Imrãn aya ta 19. Kuma ko mutum ya yarda da bautar Allah amma bai karɓi Musulunci ba, to Allah ba Zai karɓa masa ba, domin Ya ce:” Duk kuma wanda ya nemi bin wani addini ba Musulunci ba, to har abada ba za a karɓa daga gare shi ba, kuma shi a lahira yana cikin hasararru ” Suratu Ãli Imrãna aya ta 85. Wannan yana nuna cewa manufar Alƙur’ani ita ce shiryar da mutane su shiga cikin Musulunci ta hanyar yin imani da Allah da biyayya ga umarninsa.
3. Alƙur’ani A Matsayin Hujja: Saukar da Alƙur’ani yana ɗauke da cikakken tsarin rayuwa wanda yake jagorantar Musulumi a cikin dukan al’amuransu. Ya ƙunshi dokokin ibada kamar sallah da azumi da zakka da kuma hajji, da sauran su. Kuma ya ƙunshi dokokin mu’amala kamar ciniki da aure da kasuwanci, da sauran su. Hakanan Ya ƙunshi kyawawan ɗabi’u kamar gaskiya da zumunta, da , haƙuri da adalci da roƙon amana da sauran su. Kuma ya ƙunshi hukunce-hukunce da shari’a kamar halas da haram. Wannan yana nuna cewa saukar da Alƙur’ani ba wai kawai don sanin Allah ba ne, har ma don rayuwar duniya da lahira.
4. Manufar Saukar da Alƙur’ani ta Ķunshi dukan Halitta: Saukar da Alƙur’ani haske ne ga duniya baki ɗaya, mutane da aljanu, da ƙwari da dabbobi da halittu baki ɗaya, domin dukansu su san hanyar shiriya. Saboda haka, yana kira ga: da bin Alƙur’ani, kowa ya yi imani da Allah kaɗai ne abin bauta ba tare da an sanya masa kini ba. Mushrika da Ahlul Kitabi, wato Yahudu da Nasara da Maguzawa da kowa da kowa da su kaɗaita Allah da bauta, su shiga addininsa, kuma su bi shiriyarsa a kowane al’amari na rayuwarsu.
A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai tana bayani a kan cewa Alƙur’ani ya zo ne domin:
1. Kiran mutane su bauta wa Allah shi kaɗai,
2. Shiriyar da mutane zuwa ga addinin Musulunci,
3. Tabbatar da doka da tsarin rayuwa mai cike da adalci,
4. Fitar da mutane daga duhun jahilci zuwa hasken shiriya, domin samun jin daɗin duniya da lahira.
Wannan shi ne babban abin da Alƙur’ani ya zo da shi, kuma dukkan surori da ayoyinsa suna bayani ne akan waɗannan ginshiƙai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Alƙur ani ya bautar Allah
এছাড়াও পড়ুন:
Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na shiyyar Abuja (AEDC) ya fara aikin rage ma’aikata kusan 800, a daidai lokacin da ’yan Najeriya ke ci gaba da fama da hauhawar farashi, tsadar rayuwa, da rashin tabbas wajen samun wutar lantarki.
Matakin korar wanda ta fara a ranar Laraba, ya biyo bayan watanni na sake fasalin cikin gida a kamfanin da ke ba da wutar lantarki ga Babban Birnin Tarayya Abuja da jihohin Kogi, Neja da Nasarawa.
Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-AllahMajiyoyi da dama da ke da masaniya kan lamarin sun shaida cewa shugabannin kamfanin sun fara ne da shirin korar ma’aikata 1,800, kafin su rage adadin zuwa 800 bayan jerin tattaunawa masu zafi da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki da Ƙungiyoyin Kwadago.
Wata majiya daga cikin ma’aikatan AEDC ta ce shugabannin kamfanin sun fara da shirin korar 1,800, amma sun rage zuwa 800 bayan matsin lamba daga ƙungiyoyin, waɗanda a farko suka dage cewa ba a kamata a kori kowa ba.
“Shugabanni sun so su kori 1,800, amma bayan matsin lamba, sun rage zuwa 800. Tun da farko kungiyoyin sun nemi kada a kori kowa,” in ji ma’aikacin da ya nemi a boye sunansa don kauce wa hukunta shi.
“Ƙungiyoyin sun fara da cewa kada a kori kowa, amma daga baya an ce sun amince da 800. Ma’aikatan da abin ya shafa sun kamata su fara karɓar takardunsu daga ranar Litinin, amma an jinkirta, sai jiya aka fara ba su takarda,” wata majiya ta bayyana.
Wata takardar sallama mai taken “Sanarwar Sallama Daga Aiki”, da aka rubuta a ranar 5 ga Nuwamba, 2025, kuma Adeniyi Adejola, Babban Jami’in Kula da Ma’aikata na kamfanin, ya sanya wa hannu, ta tabbatar da cewa aikin na daga cikin “shirin daidaita ma’aikata da ake ci gaba da aiwatarwa.”
Takardar ta kuma bayyana cewa duk ma’aikatan da abin ya shafa za su karɓi haƙƙinsu bayan kammala tsarin sallamar su.
Wani ɓangare na takardar ya ce: “Muna bakin cikin sanar da kai cewa ba za a sake buƙatar ayyukanka a kamfanin nan ba daga ranar 5 ga watan Nuwamba, 2025. Wannan shawara ta biyo bayan sakamakon aikin daidaita ma’aikata da kamfanin ke aiwatarwa. Ka tabbata cewa an yanke wannan shawara bayan dogon nazari da kuma bisa ka’idojin kamfanin.”
“Ana buƙatar ka kammala tsarin sallama a wurin aikinka, ka kuma dawo da duk wani kayan kamfani da ke hannunka kafin ka mika kanka ga wakilin kula da ma’aikata. Kammala waɗannan matakai ne zai ba da damar sarrafa kuɗin sallamarka,” in ji takardar sallamar.