Aminiya:
2025-06-15@13:12:18 GMT

Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe

Published: 9th, March 2025 GMT

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Balanga/Billiri a Jihar Gombe, Ali Isa JC, ya raba wa Musulmai da Kiristoci 2,000 kayan abinci don rage wahalar Azumin watan Ramadan da na Kiristoci.

Ali JC ya bayyana cewa wannan tallafi yana da muhimmanci don sauƙaƙa wa jama’a gudanar da ibadarsu cikin sauƙi.

An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta

“Buƙatar kayan abinci tana ƙaruwar a irin wannan lokaci, kuma muna ƙoƙarin taimaka wa mutanen mazaɓarmu su samu sauƙin rayuwa,” in ji shi.

Baya ga kayan abinci, ya kuma raba babura 10 da babura masu kafa uku guda 20 domin tallafa wa mutane 200 a Jihar Gombe, inda kashi 50 cikin 100 aka ware wa mazaɓarsa.

Ya buƙaci waɗanda suka ci gajiyar tallafin da su kasance masu godiya, su yi addu’a domin zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

A gefe guda, ya bayyana cewa yana da muhimmanci a bar kotu ta yi aikinta kan cece-kucen da ke tsakanin Sanata Natasha Akpoti da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

“Dole ne mu bari doka ta yi aikinta ba tare da son zuciya ba,” in ji shi.

Tallafin da Ali JC ya bayar yana cikin ƙoƙarinsa na inganta rayuwar al’ummarsa da kuma tallafa wa jama’a a Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kayan abinci kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada

Kwamandan  sararin samaniya na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Janar Amir Ali Haji Zadeh yana cikin wadanda su ka yi shahada sanadiyyar harin da sojojin HKI su ka kawo wa  da asubahin yau Juma’a.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” ya nakalto majiyar juyin juya halin musulunci ta Iran tana tabbatar da shahadar Janar  Amir Ali Haji Zadeh.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara