Daga karshe Abubakar Waziri Bado ya yi kira da a maimakon malamai su koma gefe su na zagi yan fim kamata ya yi ace su shigo cikin harkar a dama dasu, domin kuwa yanzu wani lokaci ne da ake ciki inda da dama mutane sun fi kallon fina-finai fiye da yadda su ke kallon karatuttukan malaman addini, saboda haka su shigo a hada karfi da karfe wajen kara tsaftace wannan masana’antar don kuwa ni ma kaina da ace ba jarumin fim bane ni , to da tabbas zan zama malamin addinin musulunci saboda ina matukar sha’awar ganin al’umma ta gyaru.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jarumi Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC

Hukumar kare hakkin bil’adama ta kasa (NHRC) a jihar Kano ta ce ta samu rahoton laifuka 351 na take hakkin yara daga cikin jimillar kararraki 446 da ta samu daga watan Afrilu zuwa Yuni 2025.

 

Kodinetan NHRC na jihar Kano Alhaji Shehu Abdullahi ne ya bayyana haka a Kano.

 

Ya bayyana cewa daga cikin jimillar korafe-korafe 446 da aka samu a cikin watanni uku 351 na da alaka da take hakkin yara.

 

Ko’odinetan jihar ya yi nuni da cewa, sauran shari’o’in sun hada da tashin hankalin gida 19, 18 da suka shafi ‘yancin tattalin arziki da zamantakewa, da kuma biyar da suka shafi ‘yancin rayuwa.

 

 

“cikin zarge zargen har na Maita da sauran shari’o’in da suka shafi take hakkin dan adam”

 

 

A cewar Alhaji Shehu, yanayin zamantakewar al’umma a halin yanzu yana nuni da yadda ake tauye hakkin yara, wanda hakan ya nuna yadda ake kara yawaitar yaran da ke yin bara a tituna da kuma rayuwa cikin mawuyacin hali.

 

“Sakaci na iyali da al’umma shi ne babban abin da ke haifar da cin zarafin yara da kuma karuwar ayyukan aikata laifuka a tsakanin matasa.”

 

Ko’odinetan hukumar ta NHRC ya jaddada cewa, yayin da bakwai kawai daga cikin wadanda aka bayar da rahoton an aikata su ne ta hannun masu  fada aji kuma yana farywa a cikin gidajen aure.

 

“Iyali su ne tushen al’umma, al’umma kuma ita ce al’umma, saboda haka, duk wani cin zarafi a cikin iyali zai yi naso a kan al’umma baki daya.”

 

Ya kara da cewa “Lokacin da aka samu babban cin zarafi a cikin iyali, ba za a iya samun ci gaba mai ma’ana a cikin al’umma mafi girma ba.”

 

Alhaji Shehu ya ci gaba da cewa, daga cikin korafe-korafen da aka samu, an gudanar da cikakken bincike da kuma kammala shari’o’i 341, yayin da 105 ke ci gaba da sauraron karar.

 

Ya yi kira ga jama’a da su samar da zaman lafiya da juna tare da kai rahoton duk wani da ake zargi da take hakkin dan Adam ga hukumomin da abin ya shafa.

 

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, NHRC tana aiki ne a matsayin wata hanya mai zaman kanta don tabbatar da mutuntawa, kariya, da kuma inganta hakin bil’adama a Najeriya.

 

Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • Araqchi Ya Gana Da Babban Malamin Yahudawa Mai Adawa Da ‘Yan Sahayoniyya A Gefen Taron Kungiyar BRICS
  • Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
  • Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Al’ummar Iran Mabiya Imam Husain {a.s} Ba Za Su Taba Mika Kai Ga Kaskanci Ba