Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
Published: 22nd, February 2025 GMT
Sojojin kasa na jumhuriyar Musulunci ta Iran sun hada guiwa da sojojin ruwa don atisayen hadin guiwa wanda suka sanyawa suna Zulfikar 1403.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakain atisayen Brigadier General Alireza Sheikh yqana cewa a cikin wannan atisayen suna son gwada aiki tare da sojojin masu aiki a sama da na ruwa don samar da yanayi irin na yanayi yaki da gaske don fahintar da harkokin yaki suke tafiya.
General Alireza Sheikh yace a bangare na farko na wannan atisayen mun gwada yadda jiragen yakin masu saukar ungulu zasu sauka su tashi a dai dai lokacinda ake cikin budewa juna wuta da makiya.
Sannan manufar atisayen gaba daya itace samar da yanayi ta yadda bangarorin sojojin kasar zasu yi aiki tare a lokacin yaki, ko wane bangare yana aiki a bangaren da ya kore a kai amma kuma suna yakar makiyi guda.
Ya ce zasu yi amfani da jiragen yaki masu saukar ungulu, jiragen yaki na sojoji, masu saukar ungulu nau’in Cobra RH, SH da kuma AB212.. Sannan ana wannan atisayen ne a tashar jiragen ruwa na sojojin kasar dake Makron. Gabaki dayan atisayen na karkashin shi’arin Zulfikar 1403 ne.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar Ɗangote
Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas (NUPENG) ta tabbatar da cewa ta samu takardun kotu da ke hana mambobinta sayar da tikiti ko duk wani yunƙuri da zai kawo tsaikon al’amura a Matatar Ɗangote.
Shugaban NUPENG, Williams Akporeha, ya bayyana haka yayin taron manema labarai a Abuja ranar Talata, wanda aka gudanar tare da haɗin gwiwar Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Gas (PENGASSAN).
An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100Akporeha ya ce kungiyar tana mutunta doka, kuma za ta bari shari’a ta yi aikinta har sai an kammala duk wani sha’ani a kotu.
“Kamar yadda kowa ya sani, Ɗangote ya kai mu kotu, kuma yanzu mun samu umarnin kotu da ya hana mu sayar da tikiti ko datse duk wata hanya zuwa harabar matatarsa. Za mu ci gaba da kiyaye wannan doka, mu bar shari’a ta yi aikinta,” in ji shi.
Aminiya ta ruwaito yadda a makon da ya gabata, Kotu Masana’antu da ke Abuja ta bayar da umarnin wucin-gadi da ya hana kungiyar shiga yajin aiki ko tilasta wa direbobin manyan motoci rajista da ita.
Alkalin kotun, Mai Shari’a E.D. Subilim, ya bayar da wannan umarni, wanda ya shafi Kungiyar Direbobin Motoci Masu Dakon Man Fetur, inda ya hana su rufe hanyoyin Najeriya ko dakile ayyukan Matatar Ɗangote, MRS Oil Nigeria Plc, da MRS Oil and Gas Company Ltd.
A yayin taron, NUPENG ta musanta zargin cewa tana karɓar ₦50,000 daga manyan motocin da ke ɗaukar mai a daffo-daffo .
“Ba NUPENG kaɗai ke aiki a daffo-daffon ba. Akwai wasu ƙungiyoyi da ke aiki a wuraren. Don haka batun cewa NUPENG tana karɓar N50,000 ba gaskiya ba ne,” in ji Akporeha.