Sojojin kasa na jumhuriyar Musulunci ta Iran sun hada guiwa da sojojin ruwa don atisayen hadin guiwa wanda suka sanyawa suna Zulfikar 1403.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakain atisayen Brigadier General Alireza Sheikh yqana cewa a cikin wannan atisayen suna son gwada aiki tare da sojojin masu aiki a sama da na ruwa don samar da yanayi irin na yanayi yaki da gaske don fahintar da harkokin yaki suke tafiya.

General Alireza Sheikh yace a bangare na farko na wannan atisayen mun gwada yadda jiragen yakin masu saukar ungulu zasu sauka su tashi a dai dai lokacinda ake cikin budewa juna wuta da makiya.

Sannan manufar atisayen gaba daya itace samar da yanayi ta yadda bangarorin sojojin kasar zasu yi aiki tare a lokacin yaki, ko wane bangare yana aiki a bangaren da ya kore a kai amma kuma suna yakar makiyi guda.

Ya ce zasu yi amfani da jiragen yaki masu saukar ungulu, jiragen yaki na sojoji, masu saukar ungulu nau’in Cobra RH, SH da kuma AB212.. Sannan ana wannan atisayen ne a tashar jiragen ruwa na sojojin kasar dake Makron. Gabaki dayan atisayen na karkashin shi’arin Zulfikar 1403 ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawat 1 a garin Talasse, karamar hukumar Balanga.

Aikin, wanda aka kulla ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA), Bankin Duniya, da kamfanin MIDS Dynamics, na da aniyar samar da wutar lantarki ba tare da yankewa ba ga sama da gidaje 8,000 a Talasse da kauyuka makwabta, idan aka kammala shi cikin watanni huɗu.

Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

A wajen bikin kaddamar da aikin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana shi a matsayin muhimmin ci gaba a shirin gwamnatinsa na bunƙasa makamashi mai tsabta, araha da kuma dorewa.

“Wannan aiki ba kawai zai ba da haske ga gidaje ba ne kawai, zai ƙarfafa kasuwanci, ya samar da ayyukan yi, kuma ya kawo ci gaban tattalin arziki a yankin,” in ji Gwamnan.

Ya ƙara da cewa aikin ya nuna nasarar haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu wajen ci gaban fannin makamashi, tare da yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa gyare-gyaren da yake kawo wa fannin wutar lantarki, musamman Dokar Wuta ta 2023, wadda ta bai wa jihohi damar tsara hanyoyin samar da makamashinsu.

Shugaban REA, Injiniya Abba Aliyu, ya jinjina wa Gwamna Inuwa bisa hangen nesa da jajircewarsa wajen inganta makamashi a jihar, inda ya ce hukumar na shirin aiwatar da ƙarin ayyukan sola a ƙananan hukumomi 10 na jihar.

A nasa bangaren, Shugaban MIDS Dynamics, Injiniya Halis Mohammed, ya bayyana Gombe a matsayin jiha ta farko a Najeriya da ta bayar da kuɗin haɗin gwiwa don irin wannan aiki, kuma jagora a sauyin makamashi.

Shugabannin yankin, ciki har da Bala Waja, Alhaji Mohammed Danjuma Mohammed, da Dan Majalisa Musa Buba, sun gode wa Gwamnan bisa cika alkawarin da ya ɗauka, tare da alƙawarin kare aikin daga lalacewa da satar kayan aiki.

“Mun daɗe muna jiran wannan rana. Yanzu haske ya dawo cikin ƙasar Waja,” in ji ɗaya daga cikin shugabannin yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Iraki Na Samu Zaman Lafiya Kuma Tana Kokarin Kawo Karshen Zaman Sojojin Ketare A Kasar
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku a Kudancin Lebanon  
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai