HausaTv:
2025-11-08@19:46:15 GMT

Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka

Published: 22nd, February 2025 GMT

Iran ta jadadda anniyarta ta karfafa alaka da kasashen Afrika, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar.

A cikin wani sako da ya aike ta shafin X a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar, Esmaeil Baghaei, ya yi tsokaci kan ganawar da aka yi a ranar Alhamis tsakanin mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad Reza Aref da jakadun kasashen Afirka a Tehran.

Baghaei ya bayyana cewa, taron ya nuna aniyar Iran na karfafa alaka da fadada hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannoni daban-daban na moriyar juna.

A yayin ganawar, Aref ya bayyana cewa, dabarun gwamnatin Iran, karkashin shugaba Masoud Pezeshkian, ya yi daidai da ainihin manufofin Iran na inganta alaka da kasashen Afirka.

Ya jaddada manufar karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, a bangarori da dama, da kuma shiyya-shiyya.

“Idan aka yi la’akari da irin karfin da muke da shi, ta hanyar hada kai da hada albarkatunmu, za mu iya ba da gudummawa sosai ga ci gaban dangantaka da kuma yi wa jama’armu hidima,” in ji Aref.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Gasar cin kofin Afirka ta 2025 za a fafata tsakanin kasashe 24 da aka raba rukuni shida dauke da hurhudu kowanne. Da zarar an kammala fafatawar cikin rukunin, duk wadda ta yi ta daya da ta biyu za ta kai wasan zagaye na biyu wato na ‘yan 16 da kuma hudun da suka kare a mataki na uku a rukuni da maki mai yawa.

Sai dai zagaye na biyu za a buga ne ziri daya kwalle, duk wadda aka doke sai dai ta tattara kayanta zuwa gida. Gabaki dayan gasar wasanni 52 za a buga, 36 a karawar cikin rukuni da takwas a zagaye na biyu da hudu a kwata fainal da biyu a zagayen daf da karshe da neman mataki na uku da kuma wasan karshe.

 

Yadda aka raba rukunan gasar

An raba tawaga 24 da za ta buga gasar kofin Afirka zuwa rukuni shida dauke da hurhudu kowanne.

 

Rukunin A : Morocco, Mali, Zambia, Comoros. Rukunin B : Masar, Afirka ta Kudu, Angola, Zimbabwe

Rukunin C : NIjeriya, Tunisia, Uganda, Tanzania. Rukunin D : Senegal, Jamhuriyar Congo, Benin, Botswana. Rukunin E : Algeria, Burkina Faso, Ekuatorial Guinea, Sudan. Rukunin F : Ibory Coast, Kamaru, Gabon, Mozambikue

 

Kasashen da ake hasashen za su iya lashe gasar Morocco

Ita ce ta farko daga Afirka da ta kai zagayen daf da karshe a tarihi a Gasar Kofin Duniya da aka yi a Katar a 2022. Saboda haka tana sahun gaba da ake gannin za ta iya lashe kofin Afirka da take karbar bakunci. Rabon da kasar ta lashe kofin tun 1976, saboda za ta yi fatan daukar karo na biyu.

A gasar da aka yi a 2024, an yi waje da Morocco a zagaye na biyu wato ‘yan 16

Senegal

Mai rike da kofin 2022 za ta buga wasannin da kwarin gwiwa mai tarin fitattun ‘yan wasa da ke buga wasa a faɗin duniya karkashin Pape Thiaw, wanda ya maye gurbin Aliou Cissé. Senegal tana tare da tsoffin ‘yan wasanta da kuma matasan da suka hada da Sadio Mané da Kalidou Koulibaly da Edouard Mendy da Gana Gueye da Nicolas Jackson da Pape Matar Sarr da Habib Diarra da kuma Iliman Ndiaye.

Kawo yanzu Senegal ce kan gaba a yawan wasa ba tare da rahin nasara ba a duniya guda 25 sai Afirka ta Kudu da 23 da kuma Sifaniya mai wasa 22, Masar

Kasar Masar mai kofin Afirka bakwai tana cikin wadanda za su iya lashe kofin, wadda take karkashin Hossam Hassan ta yi wasa 12 a dukkan karawa ba tare da rashin nasara ba. Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Liberpool, Mohamed Salah yana daga fitattun ‘yan wasan tawagar da ake sa ran za su nuna kansa a wasannin.

 

Algeria

Mai koyar da tawagar ‘yan wasan kasar, Bladimir Petkobic yana ta kokarin ganin ya mayar da kasar kan ganiya, mai fitattun ‘yan wasa Mahrez da Slimani da kuma matasa Mohamed Amoura da Anis Hadj Moussa. Bayan da aka yi waje da Algeria karo biyu a jere bayan wasannin cikin

rukuni, kasar na fatan yin abin kirki a Morooco, kuma rabonta da kofin Afirka tun 2019.

 

Ibory Coast

Kasar Ibory Coast ce mai rike da kofin za ta yi kokarin sake lashe kofin karashin Emerse Faé. Duk da cewar ta yi rashin nasara a hannun Saliyo da Zambia, tawagar za ta Morocco da fitattun ‘yan wasa, illa dai akwai kalubale a matakin mai rike da kofin Afirka. Ibory Coast ce ta dauki kofin karo biyu daga gasar takwas a gasar cin kofin duniya daga cikin tawagogin da za su kece raini a Morocco.

 

Nijeriya

Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya wadda ta yi ta biyu a gasar da aka buga a Ibory Coast, za ta shiga wasannin da kwarin gwiwa. Super Eagles na da fitattun ‘yanwasa da suka hada da Bictor Osimhen da Lookman da Chukwueze da sauransu.

Yanzu dai hankali zai koma kan koci, Eric Chelle ko zai iya lashe kofin. Akwai Kasashen Da Ba a Saka su a lissafi saboda raunin tawagoginsu

 

Kamaru

A kodayaushe ba tabbas a Kamaru, bayan rashin jituwa tsakanin shugaban hukumar kwallon kafar kasar, Samuel Eto da Marc Brys. Sai dai kasar ta yi wasanni 12 ba tare da rashin nasara ba, kodayake ta yi tuntube a hannun tsibirin Cape Berde. Kamaru wadda ta lashe kofin sau biyar tana da gogewa a wasannin gasar.

 

Jamhuriyar Congo

Ita ma jamhuriyar Congo za ta yi fatan daukar fansa a hannun Senegal, wadda ta doke ta 3-2 a wasannin neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a badi. Ana sa ran tawagar wadda Yoane Wissa na Newcastle United da Fiston Mayele ke jan ragama, za ta so ta nunawa duniya cewar ba kanwar lasa ba ce.

 

Afirka ta Kudu

Bayan da Afirka ta Kudu ta taka rawar gani a wasannin da aka buga a 2023 da samun tikitin shiga gasar kofin duniya kai tsaye da za a yi a 2026. Afirka ta kudu na fatan nuna kwazo a wasannin da za ta fuskanta.

Kodayake yawancin ‘yan wasanta na buga wasa a gida daga Mamelodi Sundowns, duk da haka takan taka rawar gani da gagarar tawagogin da suke da fitattun ‘yan kwallon.

Za a buga gasar cin kofin Afirka a filaye tara cikin birane shida da suka hada da Rabat da Casablanca da Tangier da Agadir da Marrakech da kuma Fez. Birnin Rabat yana da manyan filaye hudu da suka hada da na Prince Moulay Abdellah Sports Compled, inda za a yi bikin bude gasar.

A Casablanca, filin Mohammed B da Wydad AC da Raja Casablanca ke wasanni, yana daga fitatcen filin da ake ji da shi a fadin kasar. Sauran biranen da za su karbi bakuncin wasannin sun hada da Tangier da Agadir da Marrakech da kuma Fez.

Jerin filayen da za a buga gasar

1 Prince Moulay Abdallah Sports Compled (Rabat)

2 Crown Prince Moulay El Hassan Sports Compled (Rabat)

3 El Barid Stadium (Rabat)

4 Olympic Anned Stadium of the Moulay Abdellah Compled (Rabat)

5 Mohammed B Stadium (Casablanca)

6 Fez Sports Compled (Fez)

7 Grand Stade de Tangier (Tangier)

8 Grand Stade de Marrakech (Marrakech)

9 Grand Stade d’Agadir (Agadir)

Me ya sa ‘Morocco ke kokarin mamaye kwallon kafar Afirka’a Getty

Kusan Shekaru 20 da suka wuce, Maroko ta rungumi wasanni, musamman kwallon kafa, ginshikin da tasirinta a Afirka da fiye da hakan. Ta hanyar karbar bakuncin gasar cin kofin Afirka, tana da niyyar karfafa kimarta a matsayin kasa ta zamani mai kwanciyar hankali da kuma hangen nesa.

Nagartattun ababen more rayuwa na zamani ( filayen wasa da sufuri da otal-otal da dai sauransu) ba wai kawai alamar nasarar tattalin arziki ba da take da shi, tana kuma gudanar da mulki mai inganci da kishin nahiyar Afirka. Maroko na son gabatar da kanta a matsayin cibiyar kwallon kafa ta Afirka, mai iya shirya wani babban wasanni na kasa da kasa mai inganci.

Batun karbar bakuncin gasar cin kofin Afrika ta 2025 a wuce wasanni.

Birnin Rabat, babban waje ne mai tasiri a harkokin diflomasiyya da kwallon kafa, ya zama abin tasiri da alfahari a duniya. Kasar ta riga ta zama hedkwatar kungiyoyin wasanni na Afirka da dama kuma ta ba da jari mai yawa a horo, ta hanyar Mohammed BI Academy ko kuma hadin gwiwa da wasu kungiyoyin Afirka.

Hadin gwiwar karbar gasar cin kofin duniya da za a yi a 2030 tare da Spain da Portugal babu shakka ya nuna yadda kasar ke da tasiri a gudanar da manyan wasannin kwallon kafa a duniya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax November 6, 2025 Wasanni Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba November 2, 2025 Wasanni Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE
  • An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa