HausaTv:
2025-08-09@05:07:15 GMT

Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka

Published: 22nd, February 2025 GMT

Iran ta jadadda anniyarta ta karfafa alaka da kasashen Afrika, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar.

A cikin wani sako da ya aike ta shafin X a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar, Esmaeil Baghaei, ya yi tsokaci kan ganawar da aka yi a ranar Alhamis tsakanin mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad Reza Aref da jakadun kasashen Afirka a Tehran.

Baghaei ya bayyana cewa, taron ya nuna aniyar Iran na karfafa alaka da fadada hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannoni daban-daban na moriyar juna.

A yayin ganawar, Aref ya bayyana cewa, dabarun gwamnatin Iran, karkashin shugaba Masoud Pezeshkian, ya yi daidai da ainihin manufofin Iran na inganta alaka da kasashen Afirka.

Ya jaddada manufar karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, a bangarori da dama, da kuma shiyya-shiyya.

“Idan aka yi la’akari da irin karfin da muke da shi, ta hanyar hada kai da hada albarkatunmu, za mu iya ba da gudummawa sosai ga ci gaban dangantaka da kuma yi wa jama’armu hidima,” in ji Aref.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Sakamakon kama Mu’azu Ɓarga, yanzu haka abokan ta’asar tasa sai tsallakewa suke domin tserewa kamun rundunar ‘yan sanda, duk da gudun da suke rundunar na ci gaba da farautarsu har kuma an samu nasarar ƙara damƙe mutane biyu cikin sama da mutane arba’in da Ɓarga ya bayyana wa ‘yan sanda. Wannan tasa a ranar Juma’ar da ta gabata Al’ummar Sheka ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Muryar Jama’ar Sheka ta ziyarci Shelkwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai domin jinjina wa ƙoƙarinsu.

Cikin shahararrun mafaɗatan da suka gamu da ajalinsu alokacin arangama daban-daban akwai matashin da ya addabi al’ummar Unguwar Ɗorayi mai Suna Barakita, sai kuma wani mai suna Khalufa ɗan unguwar Ƙofar Mazugal Da kuma wani guda da ke tafka irin wannan ta’asa a unguwar Gwammaja duk a kwaryar birnin Kano.

Yanzu haka dai a iya cewa faɗan daba da ƙwacen wayoyin gannu na neman zama ruwan dare a Jihar Kano, sai dai kuma rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ƙarƙashin Kwamiahinan da ke jagorantar operation ba sani ba sabo, ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan na Kano Abdullahi Haruna Kiyawa na ci gaba da samun nasarar kakkaɓe mafaɗatan tare da shiga lungu da saƙo domin farautar maɓarna

tan

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
  • Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
  • Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Kasashen Kungiyar OIC Dangane Da Gaza
  • Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
  • Amurka ta Fara Janye Wasu Sojojinta Daga Wurare 3 A Kasashen Iraki Da Siriya
  • Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Gaza
  • Jami’an Alhazai Sun Karrama DG Labbo Bisa Nasarar Hajjin 2025
  • Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin