Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka
Published: 22nd, February 2025 GMT
Iran ta jadadda anniyarta ta karfafa alaka da kasashen Afrika, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar.
A cikin wani sako da ya aike ta shafin X a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar, Esmaeil Baghaei, ya yi tsokaci kan ganawar da aka yi a ranar Alhamis tsakanin mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad Reza Aref da jakadun kasashen Afirka a Tehran.
Baghaei ya bayyana cewa, taron ya nuna aniyar Iran na karfafa alaka da fadada hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannoni daban-daban na moriyar juna.
A yayin ganawar, Aref ya bayyana cewa, dabarun gwamnatin Iran, karkashin shugaba Masoud Pezeshkian, ya yi daidai da ainihin manufofin Iran na inganta alaka da kasashen Afirka.
Ya jaddada manufar karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, a bangarori da dama, da kuma shiyya-shiyya.
“Idan aka yi la’akari da irin karfin da muke da shi, ta hanyar hada kai da hada albarkatunmu, za mu iya ba da gudummawa sosai ga ci gaban dangantaka da kuma yi wa jama’armu hidima,” in ji Aref.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
Iran ta kama mutane shida kan zargin kasancewa ’yan leken asiri ga Isra’ila.
Rahotannin kafofin watsa labarai na ƙasar Iran sun nuna cewa mutanen shida suna leken asiri ne ga hukumar leken asiri ta Isra’ila, Mossad, kuma an kama su ne a lardin Hamadan da ke yammacin kasar.
Ali Akbar Karimpour, wani jami’in Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa an kama “‘yan cin amanar ƙasar,” ne a garuruwan Hamadan, Razan, da Nahavand a cikin lardin.
Ya kara da cewa ana zargin su da gudanar da ayyukan ta intanet da nufin haifar da tashin hankalin jama’a, ɓata sunan gwamnatin Iran, da kuma gurɓata sunanta.”
Iran ta kama mutane da dama kuma ta kashe wasu da dama saboda leƙen asiri ga Isra’ila tun bayan fara yaƙinta da Isra’ila.