Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-30@23:23:57 GMT

Cocin Katolika Ya Yi Bikin Ma’aurata 21 A Neja

Published: 17th, February 2025 GMT

Cocin Katolika Ya Yi Bikin Ma’aurata 21 A Neja

Bishop na Cocin Katolika da ke  Kontagora, Babban Rabaran Bulus Yohanna ya gudanar da bikin aure ga ma’aurata ashirin da daya a jihar Neja.

A lokacin da yake jawabi yayin bikin daurin aurea cocin St. Mark Catholic da ke Nsanji Nkoso a karamar hukumar Magama ta jihar Neja,  Bishop din ya bayyana cewa, bai kamata masoya na zama tare ba har sai coci ya tabbatar da su a matsayin ma’aurata bayan an biya sadaki da kuma bin ka’idoji.

A cewar Most Reverend Bulus Yohanna “mafi yawansu sun fi dogaro da auren gargajiya wanda a baya ya basu damar zama tare. “Kuma muna bukatar mu tabbata cewa babu wani daga cikinsu da aka tilastawa”.

“Dole ne mu ƙarfafa su  su yi abin da ya dace musamman a matsayinmu na ’yan Katolika. Da wannan albarkar aure, wadannan ma’aurata ashirin da daya sun yi aure a bisa doka kuma a hukumance”.

Bishop Yohanna wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja, ya kara da cewa, aure alkawari ne na rayuwa wanda ya kamata a gina shi bisa soyayya

A nasa jawabin Rev. Fr. Francis Yasak Joshua,  ya bayyana cewa ma’auratan su 21 sun kammala ibadar aurensu na gargajiya musamman biyan kyaututtuka ga amare, ya ce an yi musu nasihar aure na tsawon watanni uku.

Su dai wadannan ma’aurata sun kasance tare na tsawon lokaci ba tare da coci ya tabbatar da auren nasu ba, inda wadanda suka fi dadewa tare su ne wadanda suka kwashe shekaru 24 a matsayin ma’aurata,  yayin da masu mafi karancin shekaru kuma su ne wadanda suka shekara daya.

Daya daga cikin wadanda suka dauki nauyin ma’auratan Lydia Ishaya ta bayyana jin dadinta inda ta ce “na yi matukar farin ciki,  ina kuma rokon Allah Ya  albarkaci aurensu”.

Wasu daga cikin ma’auratan sun bayyana jin dadinsu bisa yadda cocin ya tabbatar da aurensu a hukumunce.

Wasu daga cikin ma’auratan, Mista da Misis Cyprian Uche da suka kwashe shekaru 22 suna rayuwa tare, sun ce yanzu haka suna da ‘ya’ya 5, inda wasunsu sun  kammala manyan makarantun gaba da sakandire, sauran kuma suna makarantar sakandare.

Daga Aliyu Lawal

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Kasar Sin ta bullo da wani shirin bayar da tallafin kula da yara a fadin kasar wanda zai fara aiki daga shekarar 2025, a wani bangare na kokarin tallafa wa iyalai da kuma karfafa yawan haihuwa.

Shirin zai bai wa iyalai tallafin yuan 3,600, kimanin dalar Amurka 503, a kowace shekara a kan kowane yaro da bai kai shekaru uku da haihuwa ba.

Za a kebe tallafin daga cire harajin kudin shiga kuma ba za a kidaya shi a matsayin kudin shiga na iyalai ko na mutum daya ba a yayin da ake tantance masu karbar taimakon, inda abun zai zama kamar dai irin na wadanda ke karbar alawus na cin abinci ko kuma wadanda ke rayuwa cikin matsananciyar wahala. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo