Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@04:23:34 GMT

Cocin Katolika Ya Yi Bikin Ma’aurata 21 A Neja

Published: 17th, February 2025 GMT

Cocin Katolika Ya Yi Bikin Ma’aurata 21 A Neja

Bishop na Cocin Katolika da ke  Kontagora, Babban Rabaran Bulus Yohanna ya gudanar da bikin aure ga ma’aurata ashirin da daya a jihar Neja.

A lokacin da yake jawabi yayin bikin daurin aurea cocin St. Mark Catholic da ke Nsanji Nkoso a karamar hukumar Magama ta jihar Neja,  Bishop din ya bayyana cewa, bai kamata masoya na zama tare ba har sai coci ya tabbatar da su a matsayin ma’aurata bayan an biya sadaki da kuma bin ka’idoji.

A cewar Most Reverend Bulus Yohanna “mafi yawansu sun fi dogaro da auren gargajiya wanda a baya ya basu damar zama tare. “Kuma muna bukatar mu tabbata cewa babu wani daga cikinsu da aka tilastawa”.

“Dole ne mu ƙarfafa su  su yi abin da ya dace musamman a matsayinmu na ’yan Katolika. Da wannan albarkar aure, wadannan ma’aurata ashirin da daya sun yi aure a bisa doka kuma a hukumance”.

Bishop Yohanna wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja, ya kara da cewa, aure alkawari ne na rayuwa wanda ya kamata a gina shi bisa soyayya

A nasa jawabin Rev. Fr. Francis Yasak Joshua,  ya bayyana cewa ma’auratan su 21 sun kammala ibadar aurensu na gargajiya musamman biyan kyaututtuka ga amare, ya ce an yi musu nasihar aure na tsawon watanni uku.

Su dai wadannan ma’aurata sun kasance tare na tsawon lokaci ba tare da coci ya tabbatar da auren nasu ba, inda wadanda suka fi dadewa tare su ne wadanda suka kwashe shekaru 24 a matsayin ma’aurata,  yayin da masu mafi karancin shekaru kuma su ne wadanda suka shekara daya.

Daya daga cikin wadanda suka dauki nauyin ma’auratan Lydia Ishaya ta bayyana jin dadinta inda ta ce “na yi matukar farin ciki,  ina kuma rokon Allah Ya  albarkaci aurensu”.

Wasu daga cikin ma’auratan sun bayyana jin dadinsu bisa yadda cocin ya tabbatar da aurensu a hukumunce.

Wasu daga cikin ma’auratan, Mista da Misis Cyprian Uche da suka kwashe shekaru 22 suna rayuwa tare, sun ce yanzu haka suna da ‘ya’ya 5, inda wasunsu sun  kammala manyan makarantun gaba da sakandire, sauran kuma suna makarantar sakandare.

Daga Aliyu Lawal

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.

El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.

Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.

Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026