IPAC ta amince da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Katsina
Published: 17th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasa ta Ƙasa (IPAC), reshen Jihar Katsina, ta bayyana amincewarta da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.
Shugaban ƙungiyar, Alhaji Laminu Lawal Boyi, ya bayyana cewa IPAC ta gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, tare da bai wa dukkanin jam’iyyun siyasa damar shiga zaɓen.
“Baya ga shugabancina a IPAC, ni kuma shugaban jam’iyyar Accord ne, wacce ta shiga zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 34 da kujerun kansiloli 361 a faɗin jihar.
“A matsayina na ɗan takara kuma mai ruwa da tsaki, na gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen,” in ji shi.
Da yake yi wa manema labarai jawabi a ofishin IPAC da ke Kofar Durbi, a cikin garin Katsina, tare da wasu jiga-jigan ƙungiyar, Alhaji Laminu ya jaddada cewa a kowane zaɓe dole ne a samu wanda zai yi nasara da kuma wanda ba zai yi ba.
Ya yi kira ga waɗanda ba su yi nasara ba da su karɓi ƙaddara tare da duba gaba, domin siyasa ba ta ƙarewa.
Haka kuma ya shawarci waɗanda suka yi nasara da su fahimci cewa nasarar ba daga ƙarfinsu ko dabara ta fito ba, sai dai hukuncin Allah ne.
Don haka, ya buƙace su da su sauke nauyin da ke kansu cikin adalci, ba tare da nuna bambancin jam’iyya ba, domin yanzu lokaci ne na haɗin kai da ci gaban al’umma gaba ɗaya.
Alhaji Laminu ya ƙara da cewa, “Yanzu siyasa ta wuce, lokaci ne na aiki da tabbatar da ci gaban jama’a.
“Waɗanda suka samu nasara su yi mulki da adalci, su guji nuna bambanci, domin yanzu dukkanin al’umma na kallonsu a matsayin shugabanninsu, ba wai na jam’iyyarsu kaɗai ba.”
Shugaban ya yaba wa dukkanin ’yan takara da jam’iyyun siyasa da suka shiga zaɓen, tare da gode wa hukumomin da suka shirya zaɓen bisa ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da gudanar da shi cikin zaman lafiya da lumana.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa shugabanni goyon baya domin ci gaban Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amincewa gamayya Ƙungiya
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Gwamnan Jihar Filato, Barr. Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa babu wata ƙaramar hukuma a cikin jihar da ƴan ta’adda ko ƴan bindiga ke da iko da ita. Ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ƴan jarida da aka gudanar a sabon gidan gwamnati da ke Little Rayfield, Jos, a ranar Talata.
Gwamna Mutfwang ya ce gwamnatinsa ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar tsaro, musamman ta hanyar farfaɗo da rundunar tsaron cikin gida ta jihar wato Operation Rainbow, domin tallafa wa sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A FilatoYa ƙara da cewa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen ganin an dawo da zaman lafiya a sassan jihar da rikice-rikicen ƙabilanci ko na addini suka taɓa. Ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya domin tabbatar da fahimtar juna da daidaiton al’umma.
Gwamnan ya sake jaddada buƙatar kafa ƴansandan jiha, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a faɗin Nijeriya. Ya ce kafa ƴansandan jiha zai bai wa gwamnatocin jihohi damar yin tsari da ɗaukar matakan da suka dace da yanayin tsaron yankunansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp