Najeriya ta nuna adawa da wani yunkuri na sake fasalin Sashen Harkokin Siyasa, Zaman Lafiya da Tsaro na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) (PAPS), saboda damuwa game sanadin da ka iya tabarbarewar hanyoyin zaman lafiya da siyasa na kungiyar.

Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar ne ya sanar da wannan matsayi a madadin Shugaba Bola Tinubu, a lokacin da ake tattaunawa kan ssauye-sauyen kungiyar AU.

Shugaban na Najeriya ya kuma yabawa shugabanin kasashen Ruwanda Paul Kagame da William Ruto na Kenya, bisa shawarwarin da suka gabatar na kawo sauyi da nufin ganin kungiyar ta AU ta kara zage damtse wajen magance matsalolin  mambobin kungiyar.

Shugaba Tinubu ya bayyana goyon bayansa na samar da kwamitin sa ido kan shugabannin kasa da na gwamnati, wanda shugaba Ruto zai jagoranta, domin sa ido kan sauye-sauyen kungiyar ta AU.

Bugu da kari, ya amince da kudirin takaita ajandar taron kolin kungiyar AU zuwa wasu muhimman abubuwa uku.

Sai dai Tinubu ya ki amincewa da kudirin raba sashen na PAPS, wanda a halin yanzu jami’in diflomasiyyar Najeriya Ambasada Bankole Adeoye ke jagoranta, wanda a kwanan nan aka sake zabensa a karo na 2.

Tinubu ya bayar da hujjar cewa shirin sake fasalin zai haifar da kashe kudade na babu-gaira-babu dalili, da kuma kawo cikas ga wasu ayyukan da aka sa a gaba.

A yayin da yake jaddada gaskiya da kuma hada kai, Tinubu ya yi kira da a dauki matakin yin garambawul ga manufofin kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU. “Ya kamata mu maida hankali ne kan wuraren da aka riga aka cimma matsaya, maimakon kokarin kara tunkarar wasu sabbin abubuwa.” In ji shi.

Najeriya ta yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon baya ga sauye-sauyen kungiyar ta AU ba tare da bata wani lokaci ba, muddin dai sun kasance bisa gaskiya.

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: kungiyar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira

Haka kuma ya nemi kotu da ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da  kuma 1000.

Baya ga haka, ya buƙaci a umarci su da su nemi gafara ta hanyar wallafa bayani a manyan jaridu biyu na ƙasa.

Amma a zaman kotu na ranar Litinin, wanda ya shigar da ƙarar da lauyansa ba su halarci zaman kotu ba.

Lauyan da ke kare Emefiele da CBN, Mista Chikelue Amasiani, ya sanar da kotu cewa tun da aka shigar da ƙarar, mai ƙarar da lauyansa ba su nuna wata alama ta son ci gaba da shari’ar ba.

Ya roƙi kotun da ta kori ƙarar.

Mai shari’a Ekwo ya amince da buƙatar kuma ya kori ƙarar, inda ya bayyana cewa mai ƙarar zai iya dawo da ita idan ya shirya yin shari’ar da gaske.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”