Aminiya:
2025-08-02@11:40:11 GMT

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

Published: 4th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Mutanen da ke da sha’awar shiga harkar noma don sama wa kansu abin da za su ci ko kuma don samun kuɗaɗen shiga na fuskantar ƙalubale.

Wannan ƙalubale ya haɗa da ƙarancin ilimin noman, da na irin shuka, da rashin gonaki da dai sauran su.

NAJERIYA A YAU: Dalilin Da Za Mu Kashe Biliyan N2.

5 Kan Auren Zawarawa —Gwamnatin Kano

DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan batu tare da samar da hanyoyin noma ba tare da kashe kuɗi masu yawa ba.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

A bisa ƙiyasin da babban bankin Nijeriya (CBN) ya yi, ya ce; tumatirin da ake nomawa a   shekara a Nijeriya, ya kai kimanin tan miliyan 1.701, wanda kuma ake amfani da shi a shekara ya kai aƙalla tan 2.93, inda wannan adadin ya nuna cewa; a shekara, ana samun ƙarancinsa da ya kai na kimanin tan miiyan miliyan 1.2, inda kuma a duk shekara ake cike giɓin da ake da shi na wanda ake shigo da shi kimanin na ƙalla dala biliyan 2.5.

Wani ƙiyasi da kamfanin ‘Reportlinker’ ya gudanar ya ce, buƙatar tumatir a shekara , za ta ƙaru zuwa tan miliyan 3.01 a 2028.

Jerin Manyan ƙalubalen da Ke Shafar Farashin Tumatir A Nijeriya:

1- Noman Tumatir daga Kaka Zuwa Kaka:

Hakan na haifar da tsadar farashinsa da kuma ƙarancinsa, musamman duba da cewa; nomansa a Arewacin Nijeriya, na faraway ne daga watan Nuwamba zuwa watan Maris, inda hakan ya sa ba a yin noman na gajeren zango, wanda kuma farashinsa ke raguwa a daidai lokacin.

Amma a lokacin damina, farashinsa na ƙaruwa ne sakamakon yadda yake yin ƙaranci.

 

2- Cututtukan da Ke Lalata Tumatirin da Aka Shuka:

ɓarkewar cututtuka, kamar irin su Tuta da ke lalata tumatirin da aka shuka, na shafar tashin farashinsa da kuma ƙarancinsa a Nijeriya.

 

3- Rashin Kayan Adana Tumatirin da Aka Noma:

Wannan na haifar wa da manomansa yin asara bayan sun  girbe shi, inda aka ƙiyasta kashi 40 cikin 100 na Tumatirin da aka girbe, ba ya kai wa ga masu sayensa kai tsaye, musamman ganin cewa; tuni ya riga ya lalace.

 

4- Rashin Samun Bayanai daga Kasuwanni:

Wannan ƙalubale na haifar wa da manomansa asara mai yawan gaske, saboda rasahin samun bayanai daga kasuwanni kafin su kai ga shi kasuwa, domin sayarwa.

 

5- ƙarancin Kayan Nomans  Tumatir Na Zamani:

Hakan na sanya manoman tumatiri gazawar samun amfani mai yawa tare da yin asara bayan sun girbe shi.

 

6- Faɗuwar darajar Naira da ƙarancin ƴan ƙwadagon da Ake dauka Haya:

Akasarin ƴan ƙwadagon da ake dauka haya daga ƙasashen da ke maƙwabtaka da Nijeriya, don yin aiki a gonakin da aka shuka tumatir a Kudacin ƙasar, saboda faɗuwar darajar Naira, suna komawa ƙasashensu ne.

 

7-  Rashin Samar da Tsare-Tsare Masu ɗorewa Ga Fannin:

Babban bankin ƙasa (CBN) a 2013, ya gudanar da taruka iri daban-daban tare da samar da tsare-tsare masu ɗimbin yawa ga wannan fanni, bisa hadaka da Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara da Ma’aikatar Masana’antu da Zuba Hannun Jari, domin daidaita fannin na noman tumatir a faɗin wannan ƙasa, amma duk da haka, haƙan bai kai ga cimma ruwa ba.

Kazalika, a 2022 zuwa 2026, gwamnatin tarayya ta ƙirƙiro da tsari na ƙasa a kan noman wannan tumatir, musamman domin a rage asarar da manoma ke tabkawa, bayan girbi da kuma rage yawan shigo da shi daga ƙasashen ƙetare.

Sai dai, rashin wanzar da tsarin, ya sa lamarin ya koma tamkar ƴar gidan jiya.

 

8- Tsadar Kayan Noman Tumatir:

Kayan noman tumatir, musamman takin zamani da Iri, na da matuƙar tsada a Nijeriya, wanda idan manomansa suka shuka shi tare kuma girbe shi, ba sa iya samun wata ribar a zo a gani, inda hakan ke sanya farashinsa ya riƙa ƙaruwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari