A sabon rahoton 2024 da Bankin Duniya ya fitar, ya ce a kalla ‘yan Nijeriya miliyan 129 ne suke rayuwa cikin talauci, da ke nuni da cewa an samu kari fadawar mutane cikin talauci daga kaso 40.1 a 2018 zuwa kaso 56 a 2024.

Tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da ita tare da karuwar yawan jama’a cikin sauri, ya tsananta matakan talauci.

Raguwar tattalin arziki kasar ga kowane mutum, wanda ya ragu da kashi 25.04 cikin dari daga dala 2,162.6 a 2022 zuwa dala 1,621.1 a 2023, ya kara jaddada raguwar karfin saye da kuma tabarbarewar rayuwa bisa ga rahoton PWC.

Tashin farashin kayayyaki shi ne ke kan gaba wajen janyo wa tattalin arzikin Nijeriya matsaloli. Zuwa watan Disamban 2024, kason hauhawar farashin kayan masarufi ya kai zuwa kaso 34.8 lamarin da ke kara lafta wa ‘yan Nijeriya damuwuwi musamman na yadda suke kasa iya sayen ababen bukata kama daga kayan abinci, gidaje da kuma kiwon lafiya.

Daga watan Janairu zuwa Satumban 2024, sufuri da kayan abinci su ne aka samu karuwa sosai a kansu. Tashin kudin man fetur shi ne ya janyo dukkanin tashin kudin sufuri da na kayan abinci.

Karuwar farashin kayan abinci na nuni da barazanar adana abinci da ake ciki, wanda ya shafi ‘yan Nijeriya miliyan 25.1 a 2024. Sai dai rahoton na PwP ya yi gargadin cewa adadin zai iya karuwa zuwa miliyan 33.1 a 2025 muddin hauhawar farashin ya ci gaba da tashi.

Duk da cewa gwamnatin tarayya ta biyo da wasu tsare-tsaren da take ganin za su saukaka kamar karancin albashi, sai dai kaso 4.1 cikin 100 kacal na ‘yan kasar ne ke aiki, lamarin da ke nuni da cewa hakan ba zai yi tasiri ba.

Masu ruwa da tsaki sun lura da cewa lamarin karuwar masu fadawa cikin talauci lamari ne da ke bukatar daukan matakan gaggawa na shawo kan matsalolin da suka dabaibaye tattalin arziki. Duk da karuwar tattalin arzikin Nijeriya na GDP da kaso 3.0 a 2024 akwai bukatar kara himma a 2025.

Rahoton ya yi kira da a samar da ingantattun matakan kawar da fatara, gami da sa kaimi ga al’umma da gyare-gyaren tsari don magance hauhawar farashin kayayyaki da bunkasar tattalin arziki mai dorewa.

A cewar rahoton, idan ba a dauki kwakkwaran mataki ba, matsalar tattalin arzikin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fuskanta zai kara tabarbarewa tare da jefa dimbin iyalai cikin fatara da kuma kawo cikas ga ci gaban kasar na dogon lokaci.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin yan Nijeriya kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Gudanar Da Zaman Taron Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Iran Da Kasashen Nahiyar Afirka

An fara gudanar da zaman taron hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin  Iran da kasashen nahiyar Afirka karo na uku

A safiyar yau Lahadi ne aka bude zaman taron karo na uku kan harkokin tattalin arziki tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasashen Afirka a birnin Tehran, tare da halartar shugaban kasar Iran da mataimakinsa na farko da wasu tawagar jami’ai da ‘yan kasuwa daga nahiyar Afirka.

Kasar Iran tana gudanar da wannan biki ne tare da jami’an kungiyar Tarayyar Afirka, da manyan jami’ai, ministocin tattalin arziki da cinikayya, da shugabannin kungiyoyin kasuwanci, ‘yan kasuwa, masu fafutukar tattalin arziki, shugabannin bankuna, kamfanonin inshora, da na’urorin samar da kayayyaki, da daraktocin manyan kamfanoni da na kasa da kasa daga kasashen Afirka.

Taron hadin gwiwar tattalin arziki na Iran da Afirka na wakiltar wani sauyi a tsarin Iran na samar da hadin gwiwa da kasashen nahiyar ta Afirka. A Juyin lokaci a cikin hanyoyin haɗin gwiwa, nahiyar Afirka tana wakiltar wata dama ta musamman ga kasashe masu tasowa ta hanyar kasuwanci. Kasashen Afirka na bukatar su shigo da kayayyaki, da ayyuka, da kwararrun ma’aikata domin shawo kan koma bayan da suka fuskanta a tarihi, kuma Iran da alama tana iyaka kokarinta na taimakawa kasashen Afirka a wannan fanni.

A ranar Litinin ne ‘yan kasuwar za su ziyarci baje kolin Iran, kuma a ranar Talata bayan kammala wani taron karawa juna sani a zauren taron koli na tekun Fasha, za su nufi birnin Isfahan, tare da rakiyar tawagogin gwamnati da ‘yan kasuwar Afirka, inda za su gudanar da taruka na musamman da kuma ziyartar cibiyoyi da masana’antu fiye da 10 a lardin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • An Fara Gudanar Da Zaman Taron Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Iran Da Kasashen Nahiyar Afirka