Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ta Saki Bafalasdine Mafi Dadewa A Gidan Yarinta
Published: 26th, January 2025 GMT
Bayan tsawon shekaru 40 a tsare, shugaban fursunonin Falasdinawa, Mohammed Al-Tous, ya samu ‘yancinsa
Kungiyar kula fursunonin Falasdinawa da suke tsare a gidan yarin haramtacciyar kasar Isra’ila ta bayyana cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ta saki Muhammad al-Tous, wanda shi ne fursuna mafi tsufa a hannunta, tare da tasa keyar shi tare da wasu fursunoni 69 zuwa kasar Masar, a wani bangare na yarjejeniyar musayar fursunoni tsakaninta da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas.
A ranar Asabar din da ta gabata ne gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa 200 a madadin wasu mata sojoji hudu da kungiyar Hamas ke tsare da su a Zirin Gaza.
Al-Tous (mai shekaru 69) yana tsare tun 1985 kuma yana cikin kungiyar Fatah an yanke masa hukuncin daurin rai da rai kuma ya shafe shekaru 40 a jere a gidajen yarin haramtacciyar kasar Isra’ila.
An kama Al-Tous ne bayan an fafare shi a lokacin da yake cikin wata mota ta kungiyar Fatah da ta kai hare-hare da dama kan wasu wurare da dama a haramtacciyar kasar Isra’ila a yankin Beit Laham.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
Aƙalla jami’an tsaro 53 aka kashe a sassa daban-daban na Nijeriya cikin makonni biyu da suka wuce, bisa ga ƙididdigar da muka tattaro daga rahotannin kafofin yaɗa labarai.
Jami’an da abin ya shafa sun haɗa da sojoji da ’yan sanda da jami’an Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula (NSCDC), jami’an shige da fice da na kwastam, da ma jami’an sa-kai da ke taimaka wa jami’an tsaro, ciki har da ’yan sa-kai na JTF da na ƙungiyoyin tsaro na al’umma da gwamnatocin jihohi suka kafa.
Yawancin waɗanda aka kashe, ’yan bindiga ne suka halaka su yayin da suke ƙoƙarin kare al’umma a lokacin hari, yayin da wasu kuma aka kashe su ne a wuraren binciken tsaro da sansanoninsu.
Wannan adadi ya taƙaita ne kan alkulman da muka tattara daga rahotannin kafofin yaɗa labarai, bai haɗa da wasu hare-haren da ba a bayyana su ba ba.
NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a KogiWani bincike da muka gudanar a watan Disambar bara ya nuna cewa, daga watan Janairu 2023 zuwa Oktoba 2024, aƙalla jami’an ’yan sanda 229 aka kashe a faɗin ƙasar nan.
Binciken ya bayyana cewa ’yan bindiga, ’yan ƙungiyar IPOB da ’yan Boko Haram da ’yan fashi da makami da kuma ’yan ƙungiyoyin asiri ne suka kashe jami’an tsaron.
Sabbin hare-haren sun faru ne a jihohin Benue da Kogi, inda aka kashe ’yan sanda bakwai da wasu jami’an tsaro a lokuta daban-daban a ranar Juma’a da kuma jiya Lahadi.
Baya ga waɗanda aka kashe, an kuma sace wasu jami’an tsaro a harin da aka kai a Binuwai.
A ’yan kwanakin nan, Hukumar Tsaro ta DSS ta gurfanar da mutane tara a gaban kotu bisa zargin hannu a kisan gilla da aka yi a jihohin Binuwai da Filato.
An kai su gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda kuma aka tuhumi wani da ake zargi da fataucin makamai bisa mallakar bindigogi ƙirar M16 guda bakwai ba bisa ƙa’ida ba.
Cikin waɗanda aka gurfanar har da Haruna Adamu da Muhammad Abdullahi, ’yan asalin Karamar Hukumar Awe a Jihar Nasarawa, da ake tuhuma da laifuka huɗu kan kashe-kashe a Abinsi da Yelewata a Ƙaramar Hukumar Guma ta Jihar Binuwai a ranar 13 ga watan Yuni.
Haka kuma an gurfanar da Terkende Ashuwa da Amos Alede, dukkansu daga Guma, kan zargin kai farmaki don ramuwar gayya da kuma lalata dukiya, wanda ya haddasa salwantar shanu 12 a garin Ukpam.
Daga:
Sagir Kano Saleh, Abdullateef Salau, Idowu Isamotu (Abuja), Hope Abah (Makurdi), Tijjani Labaran (Lokoja) & Abubakar Akote (Minna)