An tabbatar da mutuwar mutane bakwai a wani sabon harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Garaha Lar da ke jihar Adamawa. Shugaban karamar hukumar Hong, Honarabul Usman Wa’aganda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa, wani mazaunin garin ya ɓata yayin da maharan suka lalata gidaje da kadarori.

An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur  Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi Wa’aganda ya kuma bayyana cewa, wani Ɗan banga na yankin ya mutu bayan da wani bam ya tashi a lokacin da yake ƙoƙarin tabbatar da tsaron yankin. A cewarsa, motar ‘yansandan da ke sintiri ta ofishin ‘yansanda na Garaha ita ma ta ƙone yayin da wani abun  fashewa ya fashe acikin motar amma babu wani mutum da ya rasa ransa. Shugaban ya ce, tsoron bama-baman da maharan ke amfani da su ya sanya zuwa wuraren da aka kai hare-haren ke da matukar wuya. Wa’aganda ya buƙaci a tura sojoji yankin da kuma tallafa wa waɗanda harin ya rutsa da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, Isra’ila ta kashe Falasdinawa 3 a Gaza

Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka kulla tsakanin kungiyar Hamas da Isra’ila, akalla Falasɗinawa uku sun rasa rayukansu a ranar Alhamis sakamakon hare-haren Isra’ila a Gaza, in ji majiyoyin lafiya a yankin.

Wata hukumar gwamnatin Isra’ila ta ce zai yi wuya ta buɗe iyakar Rafah da ke tsakanin Gaza da Masar don zirga-zirgar mutane.

Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano

Tuni dai Ministan tsaron Isra’ila ya umarci rundunar sojin kasar da ta yi kwakkwaran shiri don murkushe Hamas muddin ta karya yarjejeniyar tsagaita wutar.

A nata bangaren, Hamas ta mayar da gawarwakin wasu Isra’ilawa biyu da ta kama, amma ta amince cewa tana bukatar kayan aiki na musamman da taimako don gano sauran gawarwakin da ke cikin baraguzan gine-gine.

Ya zuwa yanzu, yakin Isra’ila a Gaza ya kashe akalla mutane 67,967 tare da jikkata 170,179 tun daga Oktoba 2023.

A Isra’ila kuma, mutane 1,139 ne suka mutu a harin ranar 7 ga watan Oktoba, 2023, kuma aka kama kimanin 200.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe
  • Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
  • Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, Isra’ila ta kashe Falasdinawa 3 a Gaza
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.