An tabbatar da mutuwar mutane bakwai a wani sabon harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Garaha Lar da ke jihar Adamawa. Shugaban karamar hukumar Hong, Honarabul Usman Wa’aganda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa, wani mazaunin garin ya ɓata yayin da maharan suka lalata gidaje da kadarori.

An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur  Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi Wa’aganda ya kuma bayyana cewa, wani Ɗan banga na yankin ya mutu bayan da wani bam ya tashi a lokacin da yake ƙoƙarin tabbatar da tsaron yankin. A cewarsa, motar ‘yansandan da ke sintiri ta ofishin ‘yansanda na Garaha ita ma ta ƙone yayin da wani abun  fashewa ya fashe acikin motar amma babu wani mutum da ya rasa ransa. Shugaban ya ce, tsoron bama-baman da maharan ke amfani da su ya sanya zuwa wuraren da aka kai hare-haren ke da matukar wuya. Wa’aganda ya buƙaci a tura sojoji yankin da kuma tallafa wa waɗanda harin ya rutsa da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara

Rundunar ’yan sandan yankin Babban Birnin Tarayya Abuja ta kama wani mutum mai suna Ahmed Abubakar mai shekara 32, bisa zargin ƙoƙarin kai harsasai 1,000 ga ’yan bindiga a Jihar Zamfara.

Kwamishinan ’yan sanda na birnin, Miller G. Dantawaye, ne ya bayyana hakan ga ’yan jarida a hedikwatar rundunar a Abuja ranar Laraba.

Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa

Dantawaye ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Litinin da misalin ƙarfe 3:30 na yamma, kuma tawagar musamman ta rundunar ce ta kama shi bayan samun sahihin bayanan sirri a Unguwar Dodo da ke ƙaramar hukumar Gwagwalada.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana mu’amala da wani abokinsa da aka gano sunansa Yusuf Mohammed, inda aka gano cewa yana shirin sayo harsasai 1,000 domin kai wa ’yan bindiga da ke cikin daji a Zamfara.

“Bincikenmu ya ƙara nuna cewa wani ɗan uwansa, Ahmed Yakubu, ne ya turo shi kuma yanzu ya cika wandonsa da iska, domin ya sayo ya kuma kai wa ’yan ta’adda da ke aiki a yankin su na Zamfara,” in ji CP Dantawaye.

Ya ce wanda ake zargin yana hannun ’yan sanda a halin yanzu, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kama abokin aikin nasa da ya tsere.

Kwamishinan ya jaddada kudirin rundunar na kawar da masu aikata laifuka a Abuja da kewaye, tare da tabbatar da tsaron mazauna yankin.

Ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda ta hanyar bayar da rahoton duk wani abin da ake zargin laifi ta layukan gaggawa na rundunar.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
  • Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahadi A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda