An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
Published: 16th, April 2025 GMT
An tabbatar da mutuwar mutane bakwai a wani sabon harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Garaha Lar da ke jihar Adamawa. Shugaban karamar hukumar Hong, Honarabul Usman Wa’aganda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa, wani mazaunin garin ya ɓata yayin da maharan suka lalata gidaje da kadarori.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
Mutane 7 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu goma sha daya suka samu munanan raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a unguwar Essa dake kan titin Agaie Badeggi a karamar hukumar Katcha a jihar Neja.
Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, NSEMA Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar hatsarin a wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a Minna.
A cewar Abdullahi Baba Arah, motar na dauke da hatsin gwamnatin tarayya, da kuma wata mota dake dauke da wasu fasinjoji 36, wadanda dukkansu maza ne zasu jihar Kano daga jihar Legas suka yi toho mu gama a lokacin da hatsarin ya afku.
Hatsarin ya afku ne da misalin karfe uku na safiyar yau, sakamakon rashin kyawun hanya a layin Lambata, Bida.
Ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, an tabbatar da mutuwar mutane 7, 11 da suka samu munanan raunuka, yayin da mutane 5 suka samu kananan yara.
Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an kai su cibiyoyin lafiya na Badeggi da Agaie, wasu kuma abokan aikinsu sun tafi da su yayin da ‘yan uwansu kuma suka tafi da wadanda suka mutu domin yi musu jana’iza.
A halin da ake ciki dai hukumar NSEMA ta gudanar da aikin bincike da ceto tare da matafiya da wasu mutanen kauyen da ke kusa da inda lamarin ya faru.
PR ALIYU LAWAL