Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

 

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

 

Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

 

Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

 

Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

 

Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hadari

এছাড়াও পড়ুন:

Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas

Hukumar Kwastam, ta kama kilo 25.5 na hodar iblis a wani jirgin ruwa na ƙasar Brazil mai suna MV San Anthonio a tashar jirgin ruwa ta Legas.

An ɓoye hodar cikin ƙananan jakunkuna biyar.

’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati

Kwanturola Emmanuel Oshoba, ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun bayanan sirri tare da haɗin gwiwar hukumar NDLEA.

Ya ƙara da cewa jirgin ya tsaya a ƙasashen da suka yi ƙaurin suna wajen harkar safarar miyagun ƙwayoyi kafin isowarsa Najeriya.

An tsare jirgin, sannan an miƙa hodar da aka kama ga NDLEA domin ci gaba da bincike.

Oshoba, ya ce wannan nasara tana nuna jajircewar hukumar Kwastam wajen kawar da haramtattun kasuwanci da kuma kare ƙasa, musamman lokacin bukukuwan ƙarshen shekara ke ƙaratowa.

Ya yi gargaɗin cewa hukumar ba za ta bari a yi amfani da ita wajen aikata laifuka ba, kuma duk kayayyakin da suka shigo da su sai an yi bincike a kansu.

A cewarsa, haɗin kai tsakanin Kwastam da NDLEA yana bayar da kyakkyawan sakamako, kuma zai ci gaba da karya tsarin masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Jami’an NDLEA ƙarƙashin jagorancin CN Haliru Umar sun karɓi kayan da aka kama.

Kwastam ta kuma buƙaci masu mu’amala da tashar su kasance masu bin doka tare da kai rahoton duk wani abun zargi domin tabbatar da tsaron tashar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja
  • Jirgin NAF ya yi hatsari a Neja
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda 20, kwangilolin haɗin gwiwa na fasaha guda biyar
  • Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi