Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

 

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

 

Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

 

Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

 

Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

 

Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hadari

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe

Wani mutum ya mutu, wasu da dama kuma sun jikkata lokacin da wata tirela ta yi karo da wata mota ƙirar akori kura Mitsubishi Canter a Damagum da misalin ƙarfe 12:50 na tsakar dare a ranar Laraba.

Kamar yadda kakakin rundunar ‘Yan sanda Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya ce tirelar, mai lambar rajista MUS 791 XH, wacce Aliyu Muhammad, mai shekara 30, daga Azare, ƙaramar hukumar Katagum, Jihar Bauchi ke tuƙawa tana tafiya daga Damaturu zuwa Legas lokacin da motar ta kufcewa direban ta afka wa motar da ke gabanta.

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Motar, mai mutane 18 da ke ciki da lamba AA 641 PKM, wadda Usman Muhammad, mai shekara 40 daga ƙauyen Yaskawel ne ke tuƙa ta.

Mai magana da yawun rundunar ya ce, an tabbatar da mutuwar fasinja ɗaya, Ɗahiru Maikuɗi mai shekara 40, daga ƙauyen Yaskawel, a babban asibitin Damagum yayin da wasu da dama suka jikkata.

A cewar rundunar, an tura waɗanda abin ya shafa shida zuwa asibitin Koyarwa da ke Damaturu don ƙarin kula da lafiyar su.

Hatsarin ya haifar da zanga-zanga daga matasan Damagum waɗanda suka koka game da yawan haɗurra a kan babbar hanyar Damaturu zuuwa Potiskum, musamman kusa da Damagum inda ake harkokin kasuwanci da zirga-zirgar masu sufuri a ƙasa ke ƙaruwa musamman a ranakun Lahadi da Laraba.

Jami’an ‘yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zangar don hana cin zarafin da ake yi wa mutane.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, Emmanuel Ado ya yi wa iyalan wanda ya rasu ta’azɗiyar rashin mamacin ya jajantawa waɗanda suka jikkata yayin wannan hatsari  yana mai umurtar Jami’in ‘yan sandan yankin da ya yi aiki tare da ƙaramar hukumar kan matakan kariya na dogon lokaci.

Ya gargaɗi masu ababen hawa game da yin gudun wuce ƙima kuma ya yi kira da a bi ƙa’idodin zirga-zirga sosai, yana mai gargaɗin cewa, waɗanda suka karya doka za su fuskanci hukunci.

Kwamishinan ya kuma shawarci mazauna yankin da su guji yin harkokin kasuwanci kusa da babbar hanyar don rage ƙarin faruwar haɗurra.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta