Mutum Shida Sun Mutu A Hatsarin Jirgi Mai Saukar Ungulu A Amurka
Published: 11th, April 2025 GMT
Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.
Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.
Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.
Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.
Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.
Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hadari
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka
Wani matashi mai shekaru 27, Chukwuebuka Eweni, ya shiga hannun ’yan sanda a birnin New Orleans na ƙasar Amurka, kan zargin kashe mahaifinsa har lahira tare da jikkata ’yan uwansa mata guda biyu a gidansu da ke unguwar Pebble.
Mahaifin matashin malami ne a fannin kimiyyar kwamfuta a Jami’ar Southern ta New Orleans.
Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16Iyayen matashin waɗanda asalin ’yan Najeriya ne, sun bayyana lamarin a matsayin abin mamaki da ban tsoro.
Sun shaida cewar Chukwuebuka na fama rashin lafiyar ƙwaƙwalwa amma bai taɓa aikata wani mummunan abu ba.
Rahotanni sun nuna cewa ɗaya daga cikin ’yan matan da aka jikkata an sallame ta daga asibiti, yayin da ɗayar ke kwance tana samun kumawar likitoci.
Rundunar ’yan sandan New Orleans ta tabbatar cewa Chukwuebuka yana hannu kuma ana duba lafiyarsa, kafin kammala bincike.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:59 na daren ranar 11 ga watan Nuwamba, 2025.
’Yan sanda sun samu kiran agajin gaggawa, inda suka garzaya gidan da lamarin ya auku suka tarar da mahaifin matashin kwance cikin jini, sannan wasu biyu sun ji rauni.
Yanzu dai ana tuhumar Chukwuebuka da laifuka biyu da suka shafi kashe mahaifinsa da kuma ƙoƙarin kashe ’yan uwansa mata guda biyu.
Ofishin Korer na Orleans Parish, zai bayyana musabbabin rasuwar mahaifin matashin bayan kammala binciken gawar.