Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

 

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

 

Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

 

Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

 

Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

 

Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hadari

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU

Kungiyar Tarayyar Turai EU ta bukaci a sake komawa teburin tattauna shirin nukiliyar Iran cikin gaggawa, inda take neman hadin kai a tsakanin Tehran da kuma Hukumar Kula da Makamashi ta Duniya IAEA.

Babbar jami’ar diflomasiyyar EU Kaja Kallas ta shaida wa Ministan Harkokin Kasashen Ketare na Iran, Abbas Aragchi cewar Brussels a shirye take ta shige gaba don ganin an koma teburin tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran bayan hare-haren Amurka a tashoshin makamashinsu.

HOTUNA: An yi jana’izar Dantata a Madina Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Bayan wata doguwar tattaunawa ta wayar tarho da jami’ar ta yi da Mista Argchi, ta wallafa a shafinta na X cewar ya kamata a koma tattaunawa kan makamashin Iran cikin gaggawa, kuma akwai bukatar hadin kai daga hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa domin cimma yarjejeniya.

Kazalika Kallas ta gargadi Tehran cewar duk wani yunkuri na janyewa daga tattaunawar ka iya dagula al’amura.

Wannan na zuwa ne bayan da Tehran ta yi watsi da sake komawa kan teburin tattaunawa da hukumar ta yi, inda Tehran ta ce tana bukatar tabbacin Amurka ba za ta sake kai mata hari ba.

A baya dai EU ta kasance mai shiga tsakani a yarjejeniyar nukiliyar Iran na 2015 da aka cimma da manyan kasashen duniya, kafin daga bisani Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi watsi da yarjejeniya a shekarar 2018.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
  • Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
  • Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi
  • Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran