Netanytahu Ya Fusta Da Furucin Kasar Canada Akan Kisan Kiyashi A Gaza
Published: 11th, April 2025 GMT
Fira ministan HKI Benjamine Netanyahu ya yi suka cikin fushi saboda Fira ministan kasar Mark Carney Canada ya bayyana cewa abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.
Shi dai Fira ministan kasar Canada Mark Carney wanda ya halarci taron yankin neman zabe a garin Calgary, yayin da wani daga cikin mahalarta, ya daga murya da karfi yana fada wa Fira ministan cewa, Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.
Sai dai kuma kwana daya bayan abinda ya faru, fira ministan na kasar Canada ya lashe amansa inda ya bayyana cewa, bai ji kamlar kisan kiyashi ba, a cikin abinda aka ambata.
Wannan bai hana Fira ministan na HKI sukar takwaransa na Canada ba,tare da bayyana shi a matsayin mai kin jinin yuhudawa.
Su kuwa kungiyoyin kare hakkin bil’adama na cikin kasar Canada sun bayyana ja da bayan da Fira minstan ya yi da cewa, ba abinda za a laminta da shi ba ne, ya zama wajibi a gare shi da ya goyi bayan MDD da kungiyoyin kasa da kasa na kare hakkin bil’adama akan cewa; Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.
Alaka a tsakanin HKI da kuma kasar Canada suna kara kamari,a lokacin da kungiyoyin kasa da kasa suke kara yi wa Tel Aviv matsin lamba akan kawo karshen yakin da take yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kisan kiyashi Fira ministan kasar Canada
এছাড়াও পড়ুন:
Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
Wani sojan ko-ta-kwana na Isra’ila ya kashe kansa sakamakon tsananin firgici da damuwar da ya shiga a yaƙin Gaza wanda Isra’ila ke aikata kisan-kiyashi.
Shafin labarai na Isra’ila, Walla, ya bayyana cewa Daniel Adri mai shekaru 24, wanda ya yi aiki a Gaza da Lebanon, ya kashe kansa bayan doguwar gwagwarmayar da ya yi da matsaloli masu alaƙa da damuwa da kuma rasa abokai biyu a yaƙin na Gaza.
Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a BornoTRT ya ruwaito cewa an gano gawar sojan a cikin wani daji kusa da birnin Safed a arewacin Isra’ila bayan ya kasa samun sukuni da yadda zai yi ya magance damuwar da ya shiga.
“Ba zai iya jurewa ba kuma ya koka da ganin hotunan gawawwaki da kuma jin warin mutuwa a kullum,” in ji mahaifiyarsa.
A cewar kafafen yaɗa labarai na Isra’ila, adadin sojojin da suka kashe kansu ya ƙaru tun bayan ɓarkewar yakin Gaza a watan Oktoban 2023.
Wani rahoto daga jaridar Israel Hayom ya nuna cewa sojoji 21 sun kashe kansu a shekarar 2024.
A watan Mayu, jaridar Haaretz ta Isra’ila ta ce sojoji 42 sun kashe kansu tun bayan ɓarkewar yakin Gaza.
Duk da kiran duniya na tsagaita wuta, Isra’ila ta ci gaba da aikata kisan ƙare-dangi a Gaza, inda ta kashe fiye da mutum 57,400, yawancinsu mata da yara, tun daga watan Oktoban 2023.