Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
Published: 12th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro a kasar Pakistan sun kubutar da mutane 155 daga cikin fasinjoji kimani 450 wadanda yan bindigan daga kungiyar ‘Baloch Liberation Army (BLA) suke garkuawa da su tun jiya, wadanda suka yi barazanar kashesu, idan gwamnatin Islamabad bata biya masu bukatunsu ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar jami’an tsaro na kasar ta Pakisatan na cewa ya zuwa yanzu sun halaka yan bindiga 27.
Kafin haka dai a jiya Talata ce yan bindiga na kungiyar BLA suka tsare wani jirgin fasinja mai suna ‘Jaffar Express’ dauke da fasinjoji 450 daga garin Quetta zuwa Peshawar.
Manufar garkuwan dai ita ce neman gwamnatin Pakisatn ta bawa yankin Baluchistan na kasar Pakisatan yencin kanta a matsayin kasa mai zaman kanta.
Labarin ya ce yan bindigan sun ta da nakiya ne suka lalata layin dogon, kafin su tilastawa Jirgin tsayawa.
Ya zuwa yanzu dai yan bindigan sun kashe mutane 3 daga cikin har da direban jirgin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya
Akalla mutanen 11 ne suka mutu, wasu 29 suka jikkata, a yayin wani hari da aka kai a bakin tekun Bondi Beach da ke birnin Sydney na ƙasar Ostireliya.
’Yan bindiga sun kai harin ne a yayin da dubban jama’a ne suka taru a bakin teku domin halartar wani biki mai suna ‘Chanukah by the Sea’, wanda ke nuna fara shagulgulan Yahudawa na Hanukkah.
Rahotanni sun ce wani mutum da ake zargin ɗaya daga cikin masu harin ya mutu, yayin da wani kuma ke cikin mawuyacin hali a asibiti. ’Yan sanda biyu na cikin mutanen da suka jikkata.
Hukumomin Ostireliya sun bayyana lamarin a matsayin harin ta’addanci, tare da jaddada cewa an shirya shi ne domin kai wa al’ummar Yahudawa hari a ranar farko ta bukukuwan Hanukkah.
Taɓarɓarewar rashin tsaro ya nuna rashin shugabanci na gari — Obi Akwai fargaba kan noman ranin banaFiraministan Ostireliya, Anthony Albanese, ya yi Allah-wadai da harin, tare da cewa mummunan ta’addanci da aka aikata ya wuce tunanin ɗan adam.