Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
Published: 12th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro a kasar Pakistan sun kubutar da mutane 155 daga cikin fasinjoji kimani 450 wadanda yan bindigan daga kungiyar ‘Baloch Liberation Army (BLA) suke garkuawa da su tun jiya, wadanda suka yi barazanar kashesu, idan gwamnatin Islamabad bata biya masu bukatunsu ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar jami’an tsaro na kasar ta Pakisatan na cewa ya zuwa yanzu sun halaka yan bindiga 27.
Kafin haka dai a jiya Talata ce yan bindiga na kungiyar BLA suka tsare wani jirgin fasinja mai suna ‘Jaffar Express’ dauke da fasinjoji 450 daga garin Quetta zuwa Peshawar.
Manufar garkuwan dai ita ce neman gwamnatin Pakisatn ta bawa yankin Baluchistan na kasar Pakisatan yencin kanta a matsayin kasa mai zaman kanta.
Labarin ya ce yan bindigan sun ta da nakiya ne suka lalata layin dogon, kafin su tilastawa Jirgin tsayawa.
Ya zuwa yanzu dai yan bindigan sun kashe mutane 3 daga cikin har da direban jirgin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta samu rahoton laifuka 25 na cin zarafin mata da ƙananan yara a Ƙananan Hukumomin Jakusko, Fika, Potiskum da Tarmuwa, inda aka kama mutum 28 da ake zargi da aikata laifukan.
Kakakin rundunar, SP Abdulkarim Dungus, ya ce an kama masu laifin ne cikin watanni uku da suka wuce, a wani yunƙuri na daƙile cin zarafin mata da yara a faɗin jihar.
Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyuDaga cikin waɗanda aka kama akwai wani matashi mai shekara 23, Yusuf Garba, da ake zargi yi wa wata yarinya mai shekaru biyar fyaɗe.
An kai yarinyar asibiti sannan ana ci gaba da bincike a kan lamarin.
A wani lamari daban, an yi wa wata yarinya mai shekara 16 fyaɗe yayin da ta ke dawowa gida daga bikin Maulidi a Babbangida.
’Yan sanda sun kama mutum biyu; Audu Ado (22) da Babangida Alhaji Dawaye, inda suka amsa laifin bibiyar yarinyar har suka yi mata rauni.
Dungus, ya ce waɗanda abin ya shafa na samun kulawa, yayin da ake ci gaba da bincike a ofishin SCID kafin gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Ado, ya la’anci waɗannan mummunan laifuka, inda ya bayyana cewa rundunar za ta gabatar da rahoton bincikenta kafkn gurfanar da waɗanda ake zargin.
Ya kuma shawarci iyaye, shugabannin al’umma da ƙungiyoyi su ƙara kula da yara tare da haɗa kai da ’yan sanda domin kare su.