Gwamnatin Jigawa Za Ta Horas Da Manoman Alkama A Birnin Kudu
Published: 24th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta yi alkawarin horar da matasa da ke aikin noman alkama a karamar hukumar Birnin Kudu.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka yayin da ya kai ziyarar duba gonakin alkama a yankin.
Ya yabawa Shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr Muhammad Uba Builder bisa wannan shiri da ya bayyana a matsayin wata hanya ta samar da aikin yi ga matasa da bunkasa harkar noma.
Kazalika, a yayin ziyarar gani da ido, Malam Umar Namadi ya kuma ba da umarnin gaggauta gina katanga da kuma gina ofishin jami’an tsaro a sabuwar tashar bada ruwan sha mai amfani da hasken rana ta garin Birnin Kudu.
Kwamishinan Albarkatun Ruwa na Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya shaida wa Gwamnan cewar, an haka rijiyoyi goma sha bakwai a wurin.
A nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bayyana cewa Karamar Hukumar ta dauki matasa kimanin 170 don yin noman alkama.
Builder, ya ce daukar matasan na da nasaba da tallafawa kokarin gwamnatin jihar na tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arzikin al’umma.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Sarkin Karaye, Mai Martaba Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, ya kammala rahoton aikinsa na wucin gadi.
Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ne ya bayyana hakan a fadar Sarkin da ke Karaye.
Ya ce rahoton ya ƙunshi dukkan abubuwan da suka shafi aikin Hajji tun daga lokacin da aka ƙaddamar da kwamitin a birnin Makkah, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf.
“Rahoton ya kunshi cikakken bayani kan ayyukan da kwamitin ya gudanar zuwa yanzu, kuma zai kasance muhimmin ɓangare na rahoton ƙarshe da za a miƙa ga Gwamna,” In ji shi.
Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta rigaya ta tattara nata cikakken rahoton, wanda za a mika wa Gwamnan nan ba da daɗewa ba.
A nasa jawabin, Sarkin Karaye ya nuna godiya ƙwarai ga Gwamnan Jihar bisa amincewa da baiwa kwamitin damar gudanar da wannan aiki mai muhimmanci.
Shugaban Hukumar gudanarwa na hukumar Alhaji Yusif Lawan, ya bayyana godiya ga Sarkin Karaye bisa sadaukarwa da haɗin kai da ya bayar, wanda ya taimaka wajen samun nasarar aikin kwamitin.
Abdullahi Jalaluddeen