Gwamnatin Jigawa Ta Bada Aikin Gyaran Titin Birnin Kudu Akan Kudi Naira Biliyan 11.5
Published: 24th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana jin dadinta bisa gagarumin nasarorin da aka samu wajen aiwatar da manufofinta guda 12 don inganta rayuwar al’umma da ma ci gaban jihar baki daya.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a yayin taron wayar da kan jama’a da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.
Ya bayyana cewa shirin da ke da nufin kusantar da jama’a ga gwamnati, zai kuma tabbatar da cewa manufofi da shirye-shiryen da aka aiwatar sun dace da muradin al’umma.
Don haka Namadi ya yabawa al’ummar yankin bisa yadda suka rungumi ayyukan da gwamnatin jihar ke aiwatarwa hannu bibbiyu, tare da yin alwashin ci gaba da samar da ingantattun ayyuka.
Gwamnan ya kuma ba da tabbacin cewa, zai yi nazarin takardar da Farfesa Abubakar Sani Birnin Kudu ya gabatar mai kunshe da bukatun al’ummar karamar hukumar ta Birnin Kudu.
Shi ma da yake jawabi kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S. Mallam ya ce gwamnatin jihar ta bada kwangilar sake gina hanyar Birnin Kudu zuwa Sundimina zuwa Kiyawa, akan kudi naira biliyan 11 da miliyan 500.
A cewarsa, aikin zai hada da sanya kwalta, da gina gadoji da magudanan ruwa, da sauran abubuwan da suka kamata.
Injiniya Gambo ya yi nuni da cewa, a halin yanzu gwamnatin jihar na gudanar da ayyukan tituna da dama a karamar hukumar Birnin Kudu.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, gwamnan farar hula na farko a jihar Alhaji Ali Sa’ad Birnin Kudu ne ya kaddamar da aikin sake gina hanyar ta Birnin Kudu zuwa Sundimina, zuwa Kiyawa a hukumance.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Matawalle Ya Bada Tallafin Kudi Da Kayayyakin Abinci Ga Iyalan Marigayi Sarkin Gusau
Ministan Harkokin Tsaron Ƙasa, Dakta Bello Mohammed Matawalle, ya baiwa iyalan marigayi Sarkin Gusau, Alhaji Ibrahim Bello, gudummawar naira miliyan biyar da kuma kayan abinci, bayan rasuwarsa a ranar Alhamis da ta gabata a birnin Abuja sakamakon gajeruwar rashin lafiya.
Dakta Matawalle, ya bayyana alhininsa bisa wannan rashi na Mai Martaba.
Baya ga gudummawar kuɗi, ministan ya kuma bada buhunan shinkafa 20, gero 10, masara 10 da kuma dawa 10 ga iyalan mamacin.
Wata tawaga mai ƙarƙashin jagorancin Sanata Hassan Muhammad Nasiha, tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara a zamanin mulkin Matawalle ne suka miƙa gudummawar a madadin ministan.
Dakta Matawalle ya bayyana marigayi Sarkin Gusau a matsayin shugaba mai ɗabi’a ta gari, wanda ya kasance mai sauƙin kai da tausayi a duk tsawon mulkinsa.
Ya ambato irin jajircewarsa wajen kula da marayu da taimaka musu wajen samun ilimi, inda da dama daga cikinsu suka zama mutane masu amfani a cikin al’umma.
“Rasuwar Sarkin ta bar gibidmai wuyar cika,” in ji Matawalle, yana mai addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, tare da baiwa iyalan haƙurin jure rashin.
Da yake karɓar tawagar da gudummawar a madadin iyalan, Hakimin Sunami, Alhaji Mainasara Bello Ciroman Gusau, ya nuna godiya ga ministan bisa wannan gudummawar.
Ya ce masarautar za ta ci gaba da tunawa tare da girmama goyon bayan da Matawalle ke baiwa masarautu, musamman a lokacin da yake gwamna.
Tawagar ta haɗa da fitattun mutane irinsu Ibrahim Umar Dangaladima, Sakataren APC na Jiha; Bashir Idris Ataka, Sakataren Walwala na APC; Mallam Yusuf Idris Gusau, Sakataren Yaɗa Labarai na APC; Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, Mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa, da sauransu.
Haka kuma, Sheikh Tukur Sani Jangebe ya yi addu’ar Allah ya ji ƙan marigayi Sarkin Gusau.
Daga Aminu Dalhatu