Gwamnatin Jigawa Ta Bada Aikin Gyaran Titin Birnin Kudu Akan Kudi Naira Biliyan 11.5
Published: 24th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana jin dadinta bisa gagarumin nasarorin da aka samu wajen aiwatar da manufofinta guda 12 don inganta rayuwar al’umma da ma ci gaban jihar baki daya.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a yayin taron wayar da kan jama’a da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.
Ya bayyana cewa shirin da ke da nufin kusantar da jama’a ga gwamnati, zai kuma tabbatar da cewa manufofi da shirye-shiryen da aka aiwatar sun dace da muradin al’umma.
Don haka Namadi ya yabawa al’ummar yankin bisa yadda suka rungumi ayyukan da gwamnatin jihar ke aiwatarwa hannu bibbiyu, tare da yin alwashin ci gaba da samar da ingantattun ayyuka.
Gwamnan ya kuma ba da tabbacin cewa, zai yi nazarin takardar da Farfesa Abubakar Sani Birnin Kudu ya gabatar mai kunshe da bukatun al’ummar karamar hukumar ta Birnin Kudu.
Shi ma da yake jawabi kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S. Mallam ya ce gwamnatin jihar ta bada kwangilar sake gina hanyar Birnin Kudu zuwa Sundimina zuwa Kiyawa, akan kudi naira biliyan 11 da miliyan 500.
A cewarsa, aikin zai hada da sanya kwalta, da gina gadoji da magudanan ruwa, da sauran abubuwan da suka kamata.
Injiniya Gambo ya yi nuni da cewa, a halin yanzu gwamnatin jihar na gudanar da ayyukan tituna da dama a karamar hukumar Birnin Kudu.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, gwamnan farar hula na farko a jihar Alhaji Ali Sa’ad Birnin Kudu ne ya kaddamar da aikin sake gina hanyar ta Birnin Kudu zuwa Sundimina, zuwa Kiyawa a hukumance.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi.
Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika binciken ya baiyana cewa wadanda basu yi karatu mai zurfi ba sun fi wadanda suka yi karatu mai zurfi samun aikin yi.
NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon LafiyaWadansu dalilai ne ke kara kawo rashin aikin yi a Najeriya?
Wadansu hanyoyi za’a bi wajen magance rashin aikin yi?
Wadannan da ma wasu tambayoyi na cikin batutuwan da Shirin Najeriya A Yau zai yi duba akai.
Domin sauke shirin, latsa nan