Aminiya:
2025-11-03@13:02:48 GMT

Matar aure ta banka wa mijinta wuta

Published: 24th, February 2025 GMT

An gurfanar da wata matar aure a kotu kan zargin ta da cinna wa mijinta wuta a Jihar Kano.

Ana zargin matar ta watsa wa mijin nata fetur sannan ta cinna masa wuta ne saboda ya shiga dakin sabuwar amaryarsa, suna tattaunawa da ita.

Shaidu sun bayyana cewa wadda ake zargin ta yi aika-aikan ne bayan ta nemi mijin nata ya fito daga dakin amaryar tasa amma ya ƙi amincewa.

Magidancin ya samu munanan kuna a sakamakon wutar da matar tasa ta yi masa.

Lauyar Gwamantin Jihar Kano, Saima Garba, ta karanta wa matar takardar tuhumar aikata kisa da ake mata, amma ta musa.

Daga nan alƙalin kotun Majistare mai Lamba  25, Halima Wali, ta ba da umarnin tsare matar a gidan yari sannan ta ɗage sauraron shari’ar da makonni biyu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya matar

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza

Turkiyye na karbar bakuncin wani taron ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan halin da ake ciki a Gaza.

Wannan taron ya zo ne bayan makonni uku da fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

A cewar Turkiyya, manufar taron ita ce taimakawa wajen mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sake tabbatar da rawar da take takawa a wannan batu.

Ƙasashen musulmin dake halartar taron na yau Litini a Istanbul su ne wadanda Donald Trump ya aminta dasu don tabbatar da nasarar shirin zaman lafiya na Gaza.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyye Hakan Fidan, wanda ke karbar bakuncin takwarorinsa, ya gabatar da wannan taron a matsayin hanyar yin nazari kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, samar da matakai na gaba, da kuma daidaita su kafin tattaunawa da kasashen Yamma.

Haka kuma hanya ce ga wadannan kasashen da suka fi yawan al’ummar Musulmi su nuna jajircewarsu wajen kiyaye yarjejeniyar tsagaita wuta.

Ya bayyana tsagaita wuta a matsayin mafi rauni idan aka yi la’akari da kalubalen da mataki na biyu na shirin ke fuskanta.

Mataki na biyu na shirin na Trump ya tanadi kwance damarar makamai na kungiyar Hamas, samar da rundunar sulhu, da sauransu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza November 3, 2025 Girgizar kasa ta yi ajalin gomman mutane a Afghanistan November 3, 2025 Najeriya : tun kafin kalamman Trump muka dauki matakai November 3, 2025 Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali November 3, 2025 UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza November 3, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza November 3, 2025 El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza
  • Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza
  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai