Mun gano inda Bello Turji ya ɓoye —Sojoji
Published: 24th, February 2025 GMT
Babban Jami’in Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Emeka Onumajuru, ya bayyana cewa saura kiris su gama da jagoran ’yan ta’adda, Bello Turji.
Manjo-Janar Emeka Onumajuru ya bayyana cewa sojojin suna kan bibiyar motsin Bello Turji, kuma sun gano inda yake, amma bai yi ƙarin bayani ba.
“Babu wani kwan-gaba-kwan-baya a wurin sojoji kan maganar Bello Turji, mun gano inda maɓoyarsa take,” in ji Janar Emeka.
Ya ci gaba da cewa a halin yanzu sojoji sun riga sun rutsa Turji a maɓoyarsa, babu inda zai iya motsawa ya je, saboda tsoro
Ya bayyana haka ne a safiyar Litinin yana mai cewa kwanakon Turji sun kusa karewa.
Janar din ya bayyana haka ne a yayin hirar da gidan talabijin na Channels ya yi da shi a ranar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Maboya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
Dakarun sojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu ’yan ta’adda yayin wani samame da suka kai garin Kunchin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.
A sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis, ta ce a ranar 10 ga watan Yuni ne rundunar FANSAN YAMMA ta kashe ƙasurguman ‘yan ta’addan da suka haɗa da Auta da Abdul Jamilu da kuma Salisu.
Leroy Sane ya koma Galatasaray Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu“Waɗannan ’yan ta’adda suna da alaƙa da ayyukan tashin hankali da ta’addanci da ake yawan samu a yankin gaba ɗaya.
“Wannan farmakin dai na nuni da wani gagarumin koma baya ga masu aikata laifuka, wanda ke dagula zaman lafiya da tsaro a yankin,” in ji sanarwar.
Bayanan sirri na farko-farko sun nuna cewa an kashe ƙarin wasu shugabannin ’yan ta’adda, ciki har da wani da aka fi sani da Babaye a lokacin harin.
Kazalika, a wani lamarin daban, rahotanni sun ce an kashe Sale Ado Madele da aka fi sani da Sarki, babban ɗan shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru.
A wani lamarin mai kama da haka, sojojin sun kuma kashe wasu ’yan ta’adda goma da suka taru a kusa da wata tashar mai da ke garin Danjibga.
Ana kyautata zaton ‘yan ta’addan na cikin wani gungun hadin-gwiwa da Dogo Sule ya haɗa domin kai hari.
Rundunar sojojin Nijeriya ta ce tana ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da kuma maido da dauwamammen zaman lafiya a fadin Jihar Zamfara da yankin Arewa maso Yamma.
“Wannan aiki yana ƙara jaddada ƙudurinmu na wargaza hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda tare da gurfanar da masu aikata laifuka a gaban ƙuliya.