Aminiya:
2025-07-31@02:43:35 GMT

Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete

Published: 23rd, April 2025 GMT

Maryam Abubakar, ɗaya ce daga cikin jaruman masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood ’yan ƙalilan da suka yi nasarar bin sahun iyayensu a harkar fim.

Matashiyar jarumar, wadda aka fi sanin ta da Maryam Intete a masana’antar, ta yi bayani a kan matsayinta na wadda iyayenta suka suka a cikin cikin harkar fim.

Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A wannan tattaunawar, jarumar ta yi bayani game da gogewarta da yadda ake samun daukaka a Kannywood, da wasu abubuwa game da ita kanta da iyayenta, da kuma sana’ar fim da dai sauransu.

Wace ce Maryam Abubakar?

An haife ni ne a Kano kuma a nan na girma. Na yi makarantar firamare da sakandare duk a Kano, daga baya na koma kasar Saudiyya inda na yi shekaru masu yawa a can.

Bayan na dawo Nijeriya ne na shiga harkar wasan fim kamar yadda na riski mahaifiyata na yi.

Ina da shekaru sama da ashirin, dangina na daga cikin masu shirya fina-finai a masana’antar Kannywood.

Idan mutum zai iya cewa sana’ar fim tana gudana a jininsa, to zan iya cewa fim na gudana a jinina, domin mahaifina ya dan yi aiki a masana’antar Kannywood kafin ya daina.

Mahaifiyata kuma har yandu tana ci gaba da taka rawa sosai a harkar shirya fina-finan Hausa.

Wanann ne ya sa na ce wasan kwaikwayo yana gudana a cikin jinina.

Amma duk da haka, ban taba tunani zama ’yar fim ba duk da cewa na kasance wani bangare na rayuwata a cikin harkar ta ginu.

Abin mamaki, bayan dawowata daga Saudiyya, na fara sha’awar bin sahun iyayena a sana’ar tasu.

Ko za ki iya mana karin bayani a kan su waye iyayenki da kika ce suna harkar fim?

Kamar yadda na faɗa a baya, mahaifina ya ɗan yi aiki a masan’antar amma mutane da yawa ba za su iya tunawa da shi ba ko da na ambaci sunansa.

Mahaifiyata kuma ta kasance ginshiki mai karfi a tarihin Kannywood, har yanzu tana taka rawa sosai a masana’antar domin tarihin masana’antar fina-finan Hausa ba zai cika ba sai an ambaci sunanta da kuma rawar da ta taka wajen ci gaban masana’antar.

Ba wata ba ce illa malama Hauwa Garba wadda aka fi sani da ’Yar Auta ko Sabura a cikin shirin Gidan Badamasi.

Ni ’yarta ce kuma ko ku yarda ko kar ku yarda nagartar mahaifiyata ce ta ja ni Kanywood.

Ana girmama ni saboda kasancewarta ’yarta kuma duk sauran ’yan wasan da na hadu da su a masana’antar a shirye suke su ba ni duk wata gudummawa da goyon baya da nake bukata.

Tun yaushe kike masana’antar Kannywood?

Yanzu dai na yi fiye da shekara biyu, kuma abin al’ajabi da sha’awa, shi ne, a cikin wannan ɗan gajeren lokaci, na yi fina-finai da yawa kuma na taka rawa a cikin kusan finafinai hudu.

Haka kuma, masu shirya fina-finai a kodayaushe suna son su saka ni a finafinansu musamman idan sun fahimci cewa ni ’yar Yar Auta ce.

Bayan fina-finan da na fito a ciki, ina da sauran fina-finan da ke jira na.

Dole ne in nuna godiya ta kwarai ga furodusoshin Kannywood bisa yadda suka amince da kuma yarda da iya wasana, dole kuma in yaba wa mahaifiyata saboda ta saukaka min tafiya, ta hanyar zama abin koyi ga yawancin matasa masu basira.

Yaya za ki kwatanta ranarki ta farko a gaban kyamara?

Ko da yake ba bakon abu ba ne a gare ni, amma bai kasance mai sauki kamar yadda nake tsammani zai kasance ba.

Idan za ka iya tunawa na gaya maka cewa na taso ne a cikin dangi inda wasan kwaikwayo ya bunkasa kuma don haka na san duk abubuwan da ke ciki.

Amma ba kamar yadda nake tunani ba, rana ta farko ta tabbatar mini da cewa akwai abubuwa da yawa fiye da abin da muke tsammanin harkar fim ta kunsa.

Abun burgewa shi ne kowa a shirye yake ya taimaka min kuma ya karfafa min gwiwa domin yin nasara.

Mene ne ra’ayin mahaifiyarki yayin da kika so shiga Kannywood?

Maganganun mahaifiyata su suke kara min karfin gwiwa wajen yin gaba kuma ina ganin tasirinsu a cikin tafiyata.

Ta ce da ni, “Maryam dole ne ki girmama kowa a wannan masana’antar, su ne manyanki kuma su ma za su yi miki jagora, ki tuna fa abokan aikin mahaifiyarki ne.”

“Wannan shi ne sirrina, ina mutunta kowa da kowa a masana’antar, kuma duk sun kasance kamar dangi ne a gare ni.

Za ki iya fitowa cikin fim daya tare da mahaifiyarki?

Fitowa a fim ɗaya tare da mahaifiyata abin alfahari ne gare ni, fim shi ne sana’ar da muke yi don dogaro da kanmu, mahaifiyata ta shahara a Kannywood kuma tana da dabi’u masu kyau, da suka cancanci a yi koyi da ita.

Kowa a masana’antar yana girmama ta saboda rawar da take takawa a duk shirin da aka saka ta.

Zan iya cewa fitowata a fim daya tare da ita zai zamo abin alfahari a matsayina na jaruma, dama ce a gare ni wacce ba kowa yake da ita ba.

Babbar nasara ce a gare ni shigowata cikin masana’antar Kannywood tun mahaifiyata tana taka rawar gani a cikinta.

Wanne abu ne ba za ki taɓa mantawa ba a matsayinki na jaruma?

Abin da ba zan taɓa mantawa ba a matsayina na jaruma shi ne duk lokacin da mutane suka nuna sun san ni a matsayin ’yar ’Yar Auta.

Girmamawa da kuma nuna sanayya da suke min a matsayin ’yarta abu ne da nake kauna wanda ba zan taba mantawa da shi ba a rayuwata.

Hakan ya nuna cewa mahaifiyata shahararriya ce, ta yi shuhura sosai a duniya, ta kafa kyakkyawan tarihi da hakan ke bin ’yayanta.

Kina da shirin da kike aikinsa a halin yandu?

Eh, ina aiki a kan shirin talabijin mai dogon zango mai suna ‘Baban Yawa’, kuma kamar yadda na faɗa a baya, ina da wasu ayyuka da ke jira na, amma a yanzu ina aiki a kan shirin mai dogon zango ne kawai.

Shin Maryam tana soyayya?

A gaskiya ba na yin soyayya. Babban abin da na sa a gaba shi ne na yi shuhura a cikin masana’antar, daga baya kuma sauran wasu abubuwa su biyo baya.

Za ki ci gaba da harkar Kannywood bayan kin yi aure?

A’a, ba na tunanin ci gaba, duk lokacin da na yi aure to na bar harkar fim a Kannywood ke nan.

Mece ce shawararki ga masu tasowa a Kannywood?

Su girmama kowa, ba da yawan fina-finai da ka fito ake samun ɗaukaka ba, shahara ita ce yawan mutane da kuka yi hulɗa da su ta hanyar wasan kwaikwayo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kannywood Maryam Abubakar Maryam Intete masana antar Kannywood kamar yadda na a masana antar a Kannywood shirya fina

এছাড়াও পড়ুন:

 Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya

Wani jami’in kasar Ukiraniya ya bayyana cewa, a kalla mutane 8 ne su ka jikkata sanadiyyar munanan hare-haren da Rasha ta kai wa birnin Kiev ta hanyar amfani da makamai masu linzami.

Shugaban sha’anin tafiyar da Mulki na soja a birnin Kiev Taimur Tikatishinko ya wallafa sanarwa a shafinsa na “Telegram’ cewa; A tsakanin wadanda su ka jikkata din da akwai karamin yaro dan shekaru 3, kuma tuni an dauki mutane 4 zuwa asibiti, daya daga cikinsu yana cikin mummunan hali.

Shi kuwa magajin birnin na Kiev Fitali Kikitshiko cewa ya yi, mutanen da su ka jikkata suna zaune ne a cikin gidaje mabanbanta a unguwa daya.

Har ila yau ya kara da cea; Harin ya haddasa fashewa mai karfi wacce ta sa tagogin gidaje su ka fashe, har zuwa gine-gine masu hawa 11.

A wani labarin daga jami’an kasar ta Ukiraniya, Rasha ta kai wasu hare-haren da jirage marasa matuki a garin Kirofifitsky wanda ya haddasa fashewa mai yawa.

A cikin makwannin bayan nan dai Rasha ta tsananta kai hare-hare a fadin kasar  Ukiraniya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuki.

Tun a 2022 ne dai Rasha ta fara kai wa Ukiraniya hare-hare bisa dalilin cewa tana son shiga cikin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato.

Kasar ta Ukiraniya dai tana samun taimakon makamai da bayanai na sirri daga kungiyar ta Nato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
  • Kissoshin Kayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 122
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya