Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
Published: 17th, April 2025 GMT
Sayyid Ammar Hakim shugaban jam’iyyar ‘ تيار الحكمة الوطني’ na kasar Iraki ya bayyana cewa kasar Iraki ce kasa ta farko wacce zata amfani da tattaunawa tsakanin Iran da kasar Amurka.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto sayyid hakim yana fadar haka a jiya, ya kuma kara da cewa kasashen Iran da Iraki suna da gangantaka da musulunci makobtaka da kuma al-adu masu yawa.
A wani waje a cikin jawabinsa Hakim ya amince da ruwan da gwamnatin kasar Amurka ta taka wajen kauda tsohuwar gwamnatin kama karya na sadam Husaini. Da kuma kawo tsarin democradiyya wanda ya bawa mutanen kasar Iraki sararawa daga musibun sadam Husain a kan mutanen kasar.
Ya kuma kammala da cewa ‘amminsa shahid Bakir Hakim’ ya taba fadar cewa akwai bukatar mutanen kasar Iran su tattaunawa tsakaninsu da kasar Amurka don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp