Kungiyar Malaman Musulmi ta yi kira da a dakatar da kisan kiyashi a Gaza cikin gaggawa
Published: 3rd, April 2025 GMT
Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana cewa laifuffukan gwamnatin sahyoniyawa a Gaza sun ketare dukkanin iyakokin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen kashe-kashen mata da kananan yara da makamai masu guba, da yunwa, kishirwa, da cututtuka.
A cewar jaridar Arabi 21, kungiyar malaman musulmi ta duniya ta yi kira ga duniya da ta bayyana goyon bayanta ga al’ummar Palasdinu ta hanyar daukar matakan gaggawa da suka hada da dukkanin hanyoyin soja, tattalin arziki, da diflomasiyya mai inganci.
Dangane da haka ne kungiyar ta yi kira ga limaman masallatan Juma’a a fadin duniya da su sadaukar da hudubar sallar Juma’a na gobe don magana kan wajabcin magance wahalhalu da radadin al’ummar Palastinu da kuma bukatar kawo karshen kisan gillar da gwamnatin sahyoniya ta ke yi wa Palastinawa.
Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta jaddada a cikin wannan bayani cewa, wannan cibiyar ta bibiyi matukar damuwa da bakin ciki da kisan gilla, da laifukan yaki , da yunwa da kishirwa, da kuma gudun hijira da gwamnatin yahudawan sahyoniya tare da goyon bayan ma’abota girman kan duniya suka saka mazauna Gaza a ciki.
Kungiyar ta kuma yi kira ga kasashen duniya da kungiyoyin kare hakkin bil adama da su ci gaba da tallafawa Gaza da kuma tattara laifukan da ake aikatawa har sai an dakatar da harin, da kuma tabbatar da adalci. Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta kuma yi kira da a gudanar da jerin gwano na lumana bayan sallar Juma’a a gobe a dukkanin kasashen musulmi, domin bayyana goyon bayansu ga zirin Gaza da kuma yin Allawadai da ayyukan wuce gona da irin Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.