Kungiyar Malaman Musulmi ta yi kira da a dakatar da kisan kiyashi a Gaza cikin gaggawa
Published: 3rd, April 2025 GMT
Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana cewa laifuffukan gwamnatin sahyoniyawa a Gaza sun ketare dukkanin iyakokin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen kashe-kashen mata da kananan yara da makamai masu guba, da yunwa, kishirwa, da cututtuka.
A cewar jaridar Arabi 21, kungiyar malaman musulmi ta duniya ta yi kira ga duniya da ta bayyana goyon bayanta ga al’ummar Palasdinu ta hanyar daukar matakan gaggawa da suka hada da dukkanin hanyoyin soja, tattalin arziki, da diflomasiyya mai inganci.
Dangane da haka ne kungiyar ta yi kira ga limaman masallatan Juma’a a fadin duniya da su sadaukar da hudubar sallar Juma’a na gobe don magana kan wajabcin magance wahalhalu da radadin al’ummar Palastinu da kuma bukatar kawo karshen kisan gillar da gwamnatin sahyoniya ta ke yi wa Palastinawa.
Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta jaddada a cikin wannan bayani cewa, wannan cibiyar ta bibiyi matukar damuwa da bakin ciki da kisan gilla, da laifukan yaki , da yunwa da kishirwa, da kuma gudun hijira da gwamnatin yahudawan sahyoniya tare da goyon bayan ma’abota girman kan duniya suka saka mazauna Gaza a ciki.
Kungiyar ta kuma yi kira ga kasashen duniya da kungiyoyin kare hakkin bil adama da su ci gaba da tallafawa Gaza da kuma tattara laifukan da ake aikatawa har sai an dakatar da harin, da kuma tabbatar da adalci. Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta kuma yi kira da a gudanar da jerin gwano na lumana bayan sallar Juma’a a gobe a dukkanin kasashen musulmi, domin bayyana goyon bayansu ga zirin Gaza da kuma yin Allawadai da ayyukan wuce gona da irin Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Kungiyar malaman musulmi ta duniya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.
Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba.
Kazalika, takwaransa na sufuri, Sa’idu Ahmed Alkali ya jaddada hakan ne a yayin jawabinsa a wajen wani taron tuntuɓa tsakanin ’yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a Jihar Kaduna.
Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasaA cewar ministan, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.
Wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar ta ambato ministan yana cewa “amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100.”
A 2024 Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau ɗin.
Kazalika, ministan ya ce Gwamnatin Tarayyar ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na Jihar Borno zuwa garin Aba na Jihar Abiya.
“Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai,” in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar.
Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba.
Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.