Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
Published: 2nd, April 2025 GMT
Sanata mai wakiltar mazabar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, da aka dakatar, ta bayyana cewa “ita ba mahaukaciya ba ce”, kuma “ba ta tsoron kowa” a yayin da take jawabi ga dimbin magoya bayanta a lokacin da ta dawo gida a Ihima, karamar hukumar Okehi ta jihar Kogi a ranar Talata da yamma. Dawowarta ta zo ne a daidai lokacin da ake cike da rikicin siyasa, domin tun da farko gwamnatin jihar Kogi da rundunar ‘yansandan jihar ta kafa dokar hana tarukan jama’a, saboda dalilan tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
Hukumar dake kula da ‘yan hijira dake karkashin MDD ta sanar da cewa, mutanen yake-yake da rikice-su ka tilastawa yin hijira a duniya ya kai miliyan 122.
A yau Alhamis ne dai hukumar dake kula da ‘yan hijirar ta bayyana haka, tana kai kara da cewa; gajiyawar da aka yi na warware fadace-fadace da rikicen da suke faruwa a duniya ne su ka kara yawan ‘yan hijirar, daga ciki har da kasashen Sudan da kuma Ukiraniya.
Haka nan kuma ta ce; Tun daga 2015 ne ake samun koma baya na kudaden da ya kamata a rika bayarwa domin taimakawa ‘yan hijira.
Shugaban hukumar ‘yan hijirar ta MDD Filippo Grandi wanda ya gabatar da rahoto akan halin da ake ciki, ya yi ishara da cewa, tun daga watan Aprilu na wannan shekara ta 2025 da ake ciki an sami karuwar mutane miliyan biyu da su ka zama ‘yan hijira, duk da cewa wani adadin da ya kai mutane miliyan biyu ‘yan kasar Syria sun koma kasarsu bayan faduwar gwamnatin Basshar Asad.
Filippo Grandi ya ce rikice-rikicen kasar Myanmar, da yakin Ukiraniya da Sudan su ne ummul-haba’isin karuwar ‘yan hijirar da kuma gajiyawa wajen kawo karshen hakan.
Kasar Amurka tana cikin wadanda su ka rage yawan taimakon kudaden da suke bayarwa a harkar agaji, yayin da kasashe kamar Birtaniya da wasu kasashen turai suke bayar da kadan.