Aminiya:
2025-07-30@21:49:27 GMT

Cutar sanƙarau ta yi ajalin mutum 3 a Gombe

Published: 28th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum uku daga cikin 33 da suka kamu da cutar sanƙarau a jihar.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Habu Dahiru ne, ya bayyana hakan yayin ƙarin haske game da ɓullar cutar a jihar.

Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi

Yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, ya bayyana cewa an samu rahoton mutum 53 da ake zargi sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi hudu: Kaltungo, Yamaltu Deba, Billiri, da Gombe.

A cewarsa, an tabbatar da mutuwar mutum uku daga ƙananan hukumomin Kaltungo, Yamaltu Deba, da Billiri.

A Shongom kuwa, daga cikin mutum huɗu da ake zargi sun kamu da cutar, an tabbatar da uku na ɗauke da ita.

Sai kuma ƙananan hukumomin Dukku da Nafada, inda aka samu mutum ɗaya kowanne, amma ba a tabbatar da sun kamu ba.

Kwamishinan, ya ce gwamnatin Gombe, ta samar da magunguna kyauta domin kula da masu cutar a cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko a ƙananan hukumomi 11 na jihar.

Ya bayyana cewa alamomin cutar sun haɗa da zazzabi, ciwon wuya, da ciwon kai mai tsanani.

Ya kuma shawarci jama’a da su kiyaye tsafta, guje wa zama a ɗakuna marasa iska, da kuma nisantar masu alamomin cutar domin hana yaɗuwarta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanƙarau tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wadannan ’yan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi sun sake nuna bajintar da kasar Sin ke nunawa a fagen kere-keren mutum-mutumi masu siffar dan’adam da kuma yadda masana’antar bangarensu ke samun ci gaba cikin hanzari a kasar.

A watan Agusta mai kamawa ne kasar Sin za ta karbi bakuncin gasar wasannin motsa jiki na mutum-mutumi masu siffar dan’adam. Kuma wannan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi da aka gwabza fafatawar karshe a dandalin wasannin motsa jiki na fasahar zamani da ke birnin Beijing, wata kyakkyawar shaida ce a kan yadda kasar ta shirya wa karbar bakuncin wannan gasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano