Cutar sanƙarau ta yi ajalin mutum 3 a Gombe
Published: 28th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum uku daga cikin 33 da suka kamu da cutar sanƙarau a jihar.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Habu Dahiru ne, ya bayyana hakan yayin ƙarin haske game da ɓullar cutar a jihar.
Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a KebbiYayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, ya bayyana cewa an samu rahoton mutum 53 da ake zargi sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi hudu: Kaltungo, Yamaltu Deba, Billiri, da Gombe.
A cewarsa, an tabbatar da mutuwar mutum uku daga ƙananan hukumomin Kaltungo, Yamaltu Deba, da Billiri.
A Shongom kuwa, daga cikin mutum huɗu da ake zargi sun kamu da cutar, an tabbatar da uku na ɗauke da ita.
Sai kuma ƙananan hukumomin Dukku da Nafada, inda aka samu mutum ɗaya kowanne, amma ba a tabbatar da sun kamu ba.
Kwamishinan, ya ce gwamnatin Gombe, ta samar da magunguna kyauta domin kula da masu cutar a cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko a ƙananan hukumomi 11 na jihar.
Ya bayyana cewa alamomin cutar sun haɗa da zazzabi, ciwon wuya, da ciwon kai mai tsanani.
Ya kuma shawarci jama’a da su kiyaye tsafta, guje wa zama a ɗakuna marasa iska, da kuma nisantar masu alamomin cutar domin hana yaɗuwarta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sanƙarau tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
Jirgin saman fasinja da ke kan hanyarsa ta zuwa Landan wanda ya yi hatsari a birnin Ahmedabad na Indiya a ranar Alhamis.
Mutum ɗaya ne ya tsira daga cikin mutane 242 da ke cikin jirgin, tare da fasa gine-ginen likitoci da iyalansu.
Wani ɗan jarida na AFP ya ga gawarwakin da aka zaƙulo daga wurin da jirgin ya faɗi, da kuma bayan jirgin ƙirar Boeing 787-8 Dreamliner a rataye a gefen wani gini da ya rutsa da shi a lokacin cin abinci.
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari“Iftila’in da ya afku a Ahmedabad ya ba mu mamaki da kuma ɓacin rai. Abin takaici ne da ba za a iya cewa komai ba,” in ji Firayim Minista Narendra Modi a bayaninsa bayan jirgin Air India mai lamba 171 ya yi hatsari bayan tashinsa.
Kwamishinan ’yan sandan birnin GS Malik ya ce gawarwakin fasinjoji da waɗanda abin ya rutsa da su a ƙasa na daga cikin 204 da aka gano zuwa yanzu, yayin da ma’aikatan lafiya ke jinya da dama waɗanda suka jikkata a birnin.
Yayin da aka fara fargabar mutuwar duk wanda ke cikin jirgin, jami’in kula da lafiya na jihar Dhananjay Dwivedi ya shaida wa AFP cewa “an tabbatar da wanda ya tsira” kuma ana jinyar shi a asibiti.
Ɗan jaridar na AFP ya ga wani gini ya ƙone ƙurmus bayan faɗuwar jirgin, inda hayaƙi ya turnuke sama da wani ɓangare na jirgin a ƙasa.
“Rabin jirgin ya faɗo cikin ginin mazaunin da likitoci ke zaune tare da iyalansu,” in ji Krishna, wani likita da bai bayyana cikakken sunansa ba.
Krishna ya ce ya ga “kusan gawarwaki 15 zuwa 20 da suka ƙone”, yayin da shi da abokan aikinsa suka ceto ɗalibai kusan 15.
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Indiya ta ce, akwai mutane 242 a cikin jirgin, ciki har da matuƙan jirgi biyu da ma’aikatan cikin jirgin 10.
Kamfanin jirgin Air India ya ce, akwai fasinjojin Indiya 169 da 53 ‘yan Burtaniya da ‘yan Portugal bakwai, da kuma wani ɗan ƙasar Kanada a cikin jirgin da zai nufi filin jirgin saman Gatwick na Landan.