Idan Fubara ya yi laifi za a iya tsige shi – Wike
Published: 12th, March 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas kuma Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce idan buƙatar tsige Gwamna Siminalayi Fubara ta zama tilas za a iya yi.
Wike ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya jaddada cewa siyasa ba wasa ba ce, kuma ya kamata a bi ƙa’ida wajen tafiyar da mulki.
Hakazalika, ya soki maganar cewa ‘yan majalisa ƙalilan za su iya zama domin yin dokokin jiha.
“Siyasa ba wasa ba ce. Idan har ya aikata abin da ya cancanci a tsige shi, to sai a tsige shi. Ba laifi ba ne,” in ji Wike.
“Ba zan yarda cewa a cikin wannan ƙasa, mutane na tunanin ‘yan majalisa uku za su zauna su yi doka, sannan su ce suna shirin zuwa Kotun Ƙoli.
“Shin har yanzu muna buƙatar yin aiki?” ya tambaya.
Rigimar siyasa a Jihar Ribas ta tsananta bayan da Kotun Ƙoli ta amince da sahihancin ‘yan majalisa 27 da ke goyon bayan Wike tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan Oktoban 2024.
Har ila yau, Wike ya jinjina wa waɗanda suka ƙalubalanci abin da ya kira rashin bin doka, inda ya bayyana cewa dole ne a mutunta zaɓaɓɓun shugabanni.
“Shugabannin majalisa da ‘yan majalisa ba yara ba ne; an zaɓe su ne, kuma ba yaran kowa ba ne.
“Ya kamata a zauna da su, a gina dangantaka da su,” in ji shi.
Alaƙa dai na ci gaba da zafi tsakanin Wike da yaronsa Fubara, tun bayan da bar mulkin Jihar Ribas.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fubara Siminalayi Fubara Siyasa yan majalisa
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump
Gwamnatin kasar Amurka ta ce bata bukatar samuwar jkadan kasar Afrika ta kudu Ebrahim Rasool a kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Jumma’a, ya kuma kara da cewa Rasool mutum ne wanda yake nuna wariya, yake kuma kin Amurkawa. Don haka bama da abinda zamu tattauna da shi, kawai bama son ganinsa a cikin kasar babba.
Rubio bai bayyana dalilan daukar wannan matakin a kan jakadan ba, amma hakan ya faru ne bayan da Jakadan Rasool ya wata cibiyar bincike na Afrika ta kudu inda a jawabin da ya gabatar ya zargi shugaban kasar Amurka Donal Trump da, da samar da shirin “sake maida Amurka kasa babba” da wani shirin fifita fararem Amurka a kan sauran mutane a duniya.
Labarin ya kara da cewa tun lokacinda Trump ya sake dawowa fadar white house aka hana jakadan Afirka ta kudu a kasar ganawa da jami’an fadar white House kamar yadda ya dace. Fakon haka Amurka ta yi barazanar dakatar da tallafin da take bawa kasar Afrika ta kudu saboda karar da ta shigar kan HKI wacce ta aiwatar da kissan kiyashi kan Falasdinawa a Gaza daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 har zuwa yanzun. Banda haka kasar ta sami goyon baya daga kasashen duniya da dama. Kuma gwamnatin Amurka ta bukata Afirka ta kudu ta janye karar amma taki amincewa.
Ya zuwa yanzu dai kotun ta ICC ta fidda sammacin kama Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministansa na Tsaro Yauf Galant. Kafin haka dai Ebrahim Rasool ya taba zaman jakadan Afrika ta kudu a kasarAmurka daga shekara ta 2010-2015 a lokacin shugabancin Barak Obama