Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta jaddada kudurin ta na tabbatar da gaskiya da adalci a shirin ciyarwa na azumin watan Ramadan da ke gudana a fadin jihar.

Shugaban kwamitin duba rabon abincin buda baki kuma wakilin mazabar Kiyawa, Alhaji Yahaya Muhammad Andaza, ya bada tabbacin haka lokacin da ya kai ziyarar bazata a wasu cibiyoyin ciyarwar.

A yayin ziyarar, kwamitin ya duba yadda ake gudanar da shirin a kananan hukumomin Birniwa da Kirikasamma da Guri da Hadejia, inda aikin kwamatin ya mayar da hankali ga tantance nasarar shirin da gano matsalolin da ke bukatar gyara.

A karshen ziyarar, Alhaji Yahaya Andaza wanda shi ne mataimakin mai tsawatarwa na majalisar, ya bayyana damuwa kan wasu kura-kurai da aka samu a cibiyar bada abincin buda baki ta garin Birniwa ta Farko, inda aka gano wasu matsaloli na rashin bin cikakken tsarin rabon abincin ga masu azumi.

Sai dai kuma, ya yaba da namijin kokarin wasu daga cikin masu dafa abinci a Kirikasamma da Hadejia, da Kasuwar Kofa, da Guri, inda shirin ke tafiya da yadda yakamata.

Wani matashi mai suna Abubakar Idris da ke kula da cibiya ta biyu a garin Guri ya samu kyakkyawan yabo daga ‘yan kwamitin, bisa tsarin da ya bi, inda a cibiyarsa ake samun dafadukar shinkafa mai kyau, hade da kifi da kwai, ko naman kaza, da kuma rarraba  kunu da kosai  a kullum ga masu azumi 300.

A cewar Usman Zakar Ayuba, jami’in kula da cibiyar Hadejia, sama da mutane 8,000 ne ake sa ran za su ci moriyar shirin a kullum a karamar hukumar Hadejia kadai.

Yana mai cewar, an kara cibiyoyi guda biyar a kan guda 22 da ke aiki a mazabu 11 na karamar hukumar.

Kazalika, Shugaban kwamatin Alhaji Yahaya Andaza ya bukaci duk masu dafa abincin azumi na Gwamnatin jihar Jigawan da su kasance masu gaskiya da adalci wajen gudanar da ayyukan su, tare da yin la’akari da darajar watan Ramadan ta hanyar tabbatar da cewa mabukata sun ci moriyar shirin yadda ya kamata.

A don haka, ya gargadi duk masu kokarin yin almundahana da kayayyakin abinci da aka tanada, yana mai cewar duk wanda aka samu da laifi na rage adadin kayan abinci kamar mudu 10 na gero don kunu, da mudu 10 na shinkafa don dafa-duka, da mudu 10 na wake don kosai, zai bandana kudarsa.

Radio Nigeria, ya bamu rahoton cewar, sama da naira miliyan dubu 4 ne gwamnatin Jigawa ta ware domin a ciyar da al’ummar musulmi da ke azumtar watan Ramadan a jihar.

Kwamitin ya kuduri aniyar ci gaba da sa ido a kan duk cibiyoyin ciyarwa a fadin jihar, domin tabbatar da cewar shirin yana tafiya yadda ya kamata.

Majalisar Dokokin ta kuma jaddada aniyarta na hukunta duk wanda aka samu da laifin yin almundahana, tare da daukar matakan da za su inganta shirin.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da masu ibada a cocin Christ Apostolic Church da ke Eruku, a jihar Kwara, sun nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansar kowanne mutum da suka kama.

A cewar Faston cocin, Lawrence Bamidele, tsakanin mutane 30 zuwa 35 aka yi garkuwa da su a daren Talata lokacin da aka kai musu mummunan hari suna tsaka da ibada a cocin.

Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai

Majiyoyi daga iyalai da shugabannin al’umma sun tabbatar a ranar Alhamis cewa masu garkuwar sun fara kiran ’yan uwan waɗanda aka sace ta hanyar amfani da wayoyinsu.

Sakataren cocin, Josiah Agbabiaka, ya ce tuni aka fara tuntubar wasu daga cikin dangin wadanda aka sace din.

Ya ce, “Gaskiya ne cewa ’yan bindigar sun fara kiran ’yan uwa ta amfani da wayoyin waɗanda aka sace don neman kudin fansa,” in ji Agbabiaka.
“Abin da aka shaida mana shi ne sun raba waɗanda aka sace gida-gida. Rukunin farko na mutane 11 an nemi su biya Naira miliyan 100 kowanne.”

Basaraken gargajiya na yankin, Olori Eta, Cif Olusegun Olukotun, wanda ’yan uwansa huɗu na cikin waɗanda aka sace, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa masu garkuwar suna kiran dangin wadanda aka sace daya bayan daya.

“’Yan bindigar sun fara kiran wasu suna neman Naira miliyan 100 kan kowanne mutum. Sun ce sun raba waɗanda aka sace gida-gida, kuma suna kiran danginsu,” in ji shi.

Olukotun ya ce yana cikin cocin tare da ’yan uwansa biyar lokacin harin, inda ya ce ya tsere ta taga yayin da sauran aka tafi da su.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta ce rundunar ba ta samu wani rahoto a hukumance ba kan neman kudin fansar.

“Ba mu da masaniya kan wani neman kudin fansa ko tuntubar iyalan waɗanda aka sace,” in ji ta a ranar Alhamis.
“Dakarunmu na musamman tare da sojoji da sauran jami’an tsaro suna kan aiki don ceto waɗanda aka yi garkuwar da su.”

Ejire-Adeyemi ta ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adekimi Ojo, ya roƙi al’umma da iyalan waɗanda aka sace da su bayar da bayanan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen aikin ceto mutanen kuma a kan lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
  • Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
  • Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar.
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace
  • Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa