Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Hukunta Masu Almundahana A Shirin Ciyarwar Azumi
Published: 12th, March 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta jaddada kudurin ta na tabbatar da gaskiya da adalci a shirin ciyarwa na azumin watan Ramadan da ke gudana a fadin jihar.
Shugaban kwamitin duba rabon abincin buda baki kuma wakilin mazabar Kiyawa, Alhaji Yahaya Muhammad Andaza, ya bada tabbacin haka lokacin da ya kai ziyarar bazata a wasu cibiyoyin ciyarwar.
A yayin ziyarar, kwamitin ya duba yadda ake gudanar da shirin a kananan hukumomin Birniwa da Kirikasamma da Guri da Hadejia, inda aikin kwamatin ya mayar da hankali ga tantance nasarar shirin da gano matsalolin da ke bukatar gyara.
A karshen ziyarar, Alhaji Yahaya Andaza wanda shi ne mataimakin mai tsawatarwa na majalisar, ya bayyana damuwa kan wasu kura-kurai da aka samu a cibiyar bada abincin buda baki ta garin Birniwa ta Farko, inda aka gano wasu matsaloli na rashin bin cikakken tsarin rabon abincin ga masu azumi.
Sai dai kuma, ya yaba da namijin kokarin wasu daga cikin masu dafa abinci a Kirikasamma da Hadejia, da Kasuwar Kofa, da Guri, inda shirin ke tafiya da yadda yakamata.
Wani matashi mai suna Abubakar Idris da ke kula da cibiya ta biyu a garin Guri ya samu kyakkyawan yabo daga ‘yan kwamitin, bisa tsarin da ya bi, inda a cibiyarsa ake samun dafadukar shinkafa mai kyau, hade da kifi da kwai, ko naman kaza, da kuma rarraba kunu da kosai a kullum ga masu azumi 300.
A cewar Usman Zakar Ayuba, jami’in kula da cibiyar Hadejia, sama da mutane 8,000 ne ake sa ran za su ci moriyar shirin a kullum a karamar hukumar Hadejia kadai.
Yana mai cewar, an kara cibiyoyi guda biyar a kan guda 22 da ke aiki a mazabu 11 na karamar hukumar.
Kazalika, Shugaban kwamatin Alhaji Yahaya Andaza ya bukaci duk masu dafa abincin azumi na Gwamnatin jihar Jigawan da su kasance masu gaskiya da adalci wajen gudanar da ayyukan su, tare da yin la’akari da darajar watan Ramadan ta hanyar tabbatar da cewa mabukata sun ci moriyar shirin yadda ya kamata.
A don haka, ya gargadi duk masu kokarin yin almundahana da kayayyakin abinci da aka tanada, yana mai cewar duk wanda aka samu da laifi na rage adadin kayan abinci kamar mudu 10 na gero don kunu, da mudu 10 na shinkafa don dafa-duka, da mudu 10 na wake don kosai, zai bandana kudarsa.
Radio Nigeria, ya bamu rahoton cewar, sama da naira miliyan dubu 4 ne gwamnatin Jigawa ta ware domin a ciyar da al’ummar musulmi da ke azumtar watan Ramadan a jihar.
Kwamitin ya kuduri aniyar ci gaba da sa ido a kan duk cibiyoyin ciyarwa a fadin jihar, domin tabbatar da cewar shirin yana tafiya yadda ya kamata.
Majalisar Dokokin ta kuma jaddada aniyarta na hukunta duk wanda aka samu da laifin yin almundahana, tare da daukar matakan da za su inganta shirin.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
Ƙungiyar ɗalibai ’yan Jihar Kano ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni da ’yan Majalisar Tarayya da su kawo ƙarshen taƙaddamar Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU.
Ƙungiyar ɗaliban ta ƙasa reshen Jihar Kano (NAKS) ta roƙi shugabannin da su gaggauta aiwatar da duk mai yiwuwa domin warware taƙaddamar da ke tsakanin gwamnati da ASUU.
IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da raiAminiyar ta ruwaito cewa, ɗaliban sun yi wannan kiran ne yayin wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyar a jami’o’in Bayero da kuma North West —Mudassir Adamu Musa da Asahabulkhair Labaran Usman —suka jagoranta.
Ɗaliban sun bayyana cewa yajin aikin da ƙungiyar ASUU ke shiga lokaci zuwa lokaci a dalilin taƙaddama da gwamnati yana gurgunta makomar karatunsu da kuma ilimi a ƙasar baki ɗaya.
Ƙungiyar ɗaliban ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da cika duk wata yarjejeniyar da ta ƙulla da ASUU, tana mai cewa muddin aka samu wani abu akasin haka, to babu shakka lamarin zai ci gaba da kawo tasgaro a harkokin ilimi a faɗin ƙasar.
Ɗaliban sun tunatar da duk masu ruwa da tsakin cewa ba su halin karatu a jami’o’in masu zaman kansa ballantana fita neman ilimi a ƙasashen ƙetare irin su Birtaniya, Indiya ko Amurka kamar yadda suke gani ’ya’yan masu hannu da shuni suna yi.