An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara
Published: 9th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun harbe shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani ta Miyetti Allah reshen Jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Asabar yayin da maharan suka biyo sawunsa suka harbe shi a ƙofar gidansa da ke yankin Oke Ose na birnin Ilorin.
Malaman Tsangaya Sun Bai wa Gwamna Inuwa Lambar Yabo Ta ‘Khadimul Qur’an’ Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — RahotoMuhammad Abdullahi, wani hadimin Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq kan hulɗa da al’umma da harkokin Fulani, ya tabbatar da faruwar lamarin.
“Eh, an kashe shi jiya da daddare. Wasu ’yan bindiga ne suka harbe shi.
“A yanzu haka ana shirin yi masa jana’iza, amma tun a jiya ’yan sanda sun zo sun fara bincike.”
Sai dai mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kwara, Ejire Adeyemi Toun da wakilinmu ya tuntuɓa, ta buƙaci ya ba ta lokaci za ta waiwaye shi daga baya.
Bayanai sun ce marigayin mai shekaru 32 tsohon hadimi ne a wurin Shugaban Ƙaramar Hukumar Moro kuma ɗaya daga cikin shugabannin Matasa Fulani a Jihar Kwara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Idris Abubakar Sakaina Jihar Kwara Ƙungiyar Miyetti Allah
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Ƴan bindiga sun kai hari a makarantar Government Girls Comprehensive Senior Secondary School (GGCSS), Maga, da ke ƙaramar hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi, inda suka kashe Mataimakin Shugaban makarantar, Hassan Yakubu Makuku, tare da sace wasu ɗalibai mata da ba a san adadinsu ba. Al’ummar yankin sun ce harin ya sake tayar da hankula a garin, wanda ke fama da yawan hare-hare a kwanakin nan.
Wani mazaunin Maga, Aliyu Yakubu, ya ce maharan sun shigo makarantar ne kimanin ƙarfe 5 na safiyar Litinin, ba tare da wata ƙwaƙƙwarar musayar wuta daga jami’an tsaro ba. Ya bayyana cewa harin ya jefa mazauna yankin cikin firgici da tashin hankali, abin da ya sa jama’a ke cikin tsananin damuwa da alhini.
’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A KebbiYakubu ya ce sun harbe Shugaban Makarantar ne a lokacin da yake ƙoƙarin kare ɗalibansa daga faɗawa hannun ƴan bindigar. Ya bayyana rasuwar tasa a matsayin babban rashi ga makarantar da kuma al’ummar yankin gaba ɗaya.
ADVERTISEMENTDaily Trust ta rawaito cewa, a halin da ake ciki, babu wata sanarwa daga Rundunar ƴansanda Jihar Kebbi game da harin. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya da dama da aka yi masa ba yayin rubuta wannan rahoto.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA