Aminiya:
2025-12-13@02:25:40 GMT

An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara

Published: 9th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun harbe shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani ta Miyetti Allah reshen Jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Asabar yayin da maharan suka biyo sawunsa suka harbe shi a ƙofar gidansa da ke yankin Oke Ose na birnin Ilorin.

Malaman Tsangaya Sun Bai wa Gwamna Inuwa Lambar Yabo Ta ‘Khadimul Qur’an’ Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto

Muhammad Abdullahi, wani hadimin Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq kan hulɗa da al’umma da harkokin Fulani, ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Eh, an kashe shi jiya da daddare. Wasu ’yan bindiga ne suka harbe shi.

“A yanzu haka ana shirin yi masa jana’iza, amma tun a jiya ’yan sanda sun zo sun fara bincike.”

Sai dai mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kwara, Ejire Adeyemi Toun da wakilinmu ya tuntuɓa, ta buƙaci ya ba ta lokaci za ta waiwaye shi daga baya.

Bayanai sun ce marigayin mai shekaru 32 tsohon hadimi ne a wurin Shugaban Ƙaramar Hukumar Moro kuma ɗaya daga cikin shugabannin Matasa Fulani a Jihar Kwara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Idris Abubakar Sakaina Jihar Kwara Ƙungiyar Miyetti Allah

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya jaddada goyon bayansa ga wa’adin mulki ɗaya kacal ga gwamnonin, yana mai cewa hakan zai inganta aiki da kuma inganta harkokin mulki.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake rantsar da sababbin zaɓaɓɓun shugabannin Ƙananan hukumomi, mataimakan shugabannin, Kwamishinoni da shugabannin hukumar a ɗakin taro na Hauwa Isah Wali da ke gidan gwamnati, Minna babban birnin jihar.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya

Bago ya bayyana cewa, saboda zaɓen 2027 ne ya hana shi ya ɗauki tsauraran matakai kan wasu jami’an idan ba don zaben da ke tafe ba, yana mai cewa tsarin wa’adi ɗaya ne zai bai wa shugabanni damar yin taka-tsantsan ba tare da matsin lamba na siyasa ba.

“Ni mai goyon bayan wa’adi ɗaya ne ga gwamnoni domin abin takaicin mun dawo kan batutuwan siyasa, komai na Najeriya cike yake da siyasa, abin takaici ne!

“Akwai abubuwan da zan iya yi a yau, amma zan yi magana ne a kai bayan zaɓe. Dole ne in sallami wasu ma’aikata da ba su da amfani, amma ba zan iya ba saboda zaɓe, sun faɗi jarabawarsu da yawa, ba za a iya yi musu ƙarin girma ba, amma nauyi ne a kan tsarin. Idan da zango ɗaya ne ake yi, da na fi yanke hukunci fiye da wanda nake a yau,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin da miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji