Aminiya:
2025-07-04@01:42:23 GMT

An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara

Published: 9th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun harbe shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani ta Miyetti Allah reshen Jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Asabar yayin da maharan suka biyo sawunsa suka harbe shi a ƙofar gidansa da ke yankin Oke Ose na birnin Ilorin.

Malaman Tsangaya Sun Bai wa Gwamna Inuwa Lambar Yabo Ta ‘Khadimul Qur’an’ Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto

Muhammad Abdullahi, wani hadimin Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq kan hulɗa da al’umma da harkokin Fulani, ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Eh, an kashe shi jiya da daddare. Wasu ’yan bindiga ne suka harbe shi.

“A yanzu haka ana shirin yi masa jana’iza, amma tun a jiya ’yan sanda sun zo sun fara bincike.”

Sai dai mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kwara, Ejire Adeyemi Toun da wakilinmu ya tuntuɓa, ta buƙaci ya ba ta lokaci za ta waiwaye shi daga baya.

Bayanai sun ce marigayin mai shekaru 32 tsohon hadimi ne a wurin Shugaban Ƙaramar Hukumar Moro kuma ɗaya daga cikin shugabannin Matasa Fulani a Jihar Kwara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Idris Abubakar Sakaina Jihar Kwara Ƙungiyar Miyetti Allah

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da ƙaddamar bincike a game da harin da dakarunta suka kai kan wata cibiyar intanet da ke yankin Gaza, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar ɗimbin fararen hula a jiya Litinin.

Hukumar kare lafiyar fararen hula ta Falasɗinu, ta ce wasu daga cikin makaman da Isra’ila ta harba a jiya Litinin sun faɗa kan kasuwar kwamfuta ta ‘Al-baqa’ da ke gaɓar teku da ke birnin Gaza, kuma a wannan cibiyar kaɗai mutane 24 ne suka rasa raukansu.

Ɗaya daga cikin masu magana da yawun rundunar sojin Isra’ila ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa, tabbatas sun kai hare-hare kan wurare da dama da dakarun Hamas ke fakewa don gudanar da ayyukansu a Gaza, to amma sun ɗauki dukkanin matakan da suka wajaba domin taƙaita illolin farmakin ga fararen hula.

Ahmed al-Nayrab, mai shekaru 26 a duniya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira da rayukansu a wannan farmaki, ya ce lokacin da aka kai harin, akwai ɗimbin mutane da suka haɗa da masu shan shayi da kuma waɗanda suka zo don samun sadarwar intanet.

Ahmed ya ci gaba da cewa, “abin da ya faru a wannan wuri ba ya da bambanci da kisan kiyashi”, yana mai cewa “a duk inda ka duba sassan gaɓoɓi ne da kuma gangar jikunan mutane ne, yayin da wasu daga cikin gawarwakin ke ci da wuta kana wasu ke kwance jina-jina’’.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima
  • Hamas ta karɓi tayin tsagaita wuta a Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma