Ci Gaban Masana’antar Kannywood: Ganin Kitse Ake Wa Rogo – Mai Sana’a
Published: 2nd, February 2025 GMT
Har ila yau ya ce, idan aka yi maganar mukaman da gwamnatin tarayya da ta jihohi suka bai wa wasu daga cikinmu, ba yana nufin cewa; an taimaki masana’antar ba ne, domin kuwa; mafi yawancin wadanda suka samu wadannan mukamai, babu wani ci gaba ko hobbasa da suka yi wajen ciyar da Masana’antar Kannywood gaba.
Musa ya ce, illa kawai dai suna taimakon kansu da kuma na kusa da su, wanda kuma ba haka ya dace a ce suna yi ba, dalili kuwa shi ne, har yau babu wani daga cikin masana’antar tamu da ya taba samun wani mukamin gwamnati, ya taimaka wa ita kanta masana’antar, illa kalilan daga cikinmu.
A bangaren abokanan fada kuwa a Masana’antar Kannywood, Mai Sana’a ya ce; duk da wannan magana da yake yi a halin yanzu, babu wani a masana’antar da zai bude baki ya ce; shi ne abokin fadansa, domin kuwa dukkanin wadanda suke tare a masana’antar, yana kallonsu da mutunci duk da cewa dai wasu sun fi wasu zama mutanen kirki.
A karshe, Musa ya bayyana cewa; idan Allah ya kawo wata sana’ar da ta fi wannan harka ta fim a wajensa, zai ajiye ta a cikin lumana; ba wai don ta yi masa tsaroro ba ba, kawai dai yana fatan wata rana wani abu daban zai zo, wanda ya fi masa harkar fim din, domin babu wani mutum a duniya da ba ya son cigaba, idan kuma wannan sana’a ita ce tsira a wajensa, yana fatan mutuwa a cikinta, ba tare da ya bar ta ba.
কীওয়ার্ড: a masana antar
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Yayin da taro na biyu na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya ke kara matsowa, sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, sun nuna gamsuwa da hadin gwiwa bisa matsayin koli dake tsakanin Sin da kasashen nan biyar na yankin tsakiyar Asiya, a matsayin wata hadaka ta al’umma mai kyakkyawar makomar bil’Adama, wadda ke kara shigar da sabon kuzari, na daidaito cikin yanayin duniya dake kara shiga yanayin tangal-tangal.
Tun dai taro na farko na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya, hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen biyar ya shiga wani sabon zango na ci gaba. Har ma kuri’un na jin ra’ayin jama’a suka nuna yadda kaso 90.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, ke ganin tsarin taron shugabannin Sin da kasashen na tsakiyar Asiya ya taka rawar gani a wannan fanni.
Kazalika, kaso 92 bisa dari na ganin ta hanyar mayar da kasashen tsakiyar Asiya daya daga muhimman jigon diflomasiyyar makwaftanta, Sin ta samar da wasu damammaki ga kasashen tsakiyar Asiya, na cimma burin sauye-sauye, da ci gaba da yin babban tasiri a shiyyarsu. Yayin da yanayin yankunan Turai da Asiya ke kara sauyawa cikin hanzari, kaso 88.1 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu na ganin gina al’ummun Sin da tsakiyar Asiya masu makomar bai daya, na da muhimmancin gaske wajen karfafa tsare-tsaren kasashen tsakiyar Asiya, na samar da ‘yanci da daidaiton shiyyarsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp