Aminiya:
2025-06-15@17:40:08 GMT

An miƙa wa Majalisar Kano ƙorafin ƙara wa’adin manyan ma’aikatan gwamnati

Published: 1st, February 2025 GMT

An miƙa wa Majalisar Dokokin Kano ƙorafi kan abin da aka bayyana a matsayin ƙarin wa’adin aiki na wasu manyan jami’an gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.

A ƙunshin ƙorafin an yi zargin cewa ana ƙara wa manyan jami’an wa’adin aiki ta hanyar amfani da Dokar Zartarwa Ta 1 ta 2025, wadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanyawa hannu.

A cikin wata wasika mai kwanan wata 6 ga Janairu, 2025, Sani Usman DanAbdullo, Esq., Daraktan Gudanarwa da Harkokin Gabaɗaya na Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano (KSACA), ya buƙaci Majalisa da ta kare doka da oda, tare da dakatar da abin da ya bayyana a matsayin rashin amfani da ikon zartarwa yadda ya kamata.

An aike da ƙorafin ne zuwa ga Kakakin Majalisar, Hon. Jibrin Ismail Falgore, da kuma Shugaban Kwamitin Majalisa kan Ƙorafe-ƙorafe na Jama’a.

Takardar ta ƙalubalanci Dokar Zartarwa da aka fitar a ranar 1 ga Janairu, 2025, wadda ake zargi da bayar da ƙarin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Magatakardan Majalisa, wasu alƙalai, da ma’aikatan ɓangaren lafiya.

Ana iya tuna cewa Gwamna Yusuf ya amince da ƙarin wa’adin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, wasu Manyan Sakatarori, da manyan ma’aikatan gwamnati, wanda zai fara aiki daga 31 ga Disamba, 2024.

Gwamnan ya kare wannan mataki, yana mai cewa Dokar Buƙatar Dole (Doctrine of Necessity) ce ta tilasta hakan, yana mai dogaro da sassa 5(2) da 208 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999.

Sai dai a cikin ƙorafin, an bayyana cewa wannan umarni ya ci karo da dokokin jihar, musamman Dokar Fansho da Giratuti ta Jihar Kano (Gyara Na 5), 2024, wadda ta tanadi shekarun ritaya su kasance shekara 60 ko shekaru 35 na aiki.

Ƙorafin ya jaddada cewa umarnin zartarwa ba domin soke doka ba ne, balle gyaranta, sai dai aiwatar da ita.

Bugu da ƙari, mai ƙorafin ya yi watsi da dogaron gwamnan kan Dokar Buƙatar Dole, yana mai bayyana hakan a matsayin maras inganci a doka da harkokin gudanarwa.

Ya gargaɗi cewa wannan umarni na iya haifar da rikice-rikicen gudanarwa, zarge-zargen nuna wariya, da kuma ƙarar da ka iya gurgunta tafiyar da mulki.

Har ila yau, ƙorafin ya caccaki tsarin zaɓaɓɓen ƙarin wa’adin ga wasu mutane kawai, yana mai cewa Jihar Kano na da ƙwararrun ma’aikata da za su iya maye gurbin waɗanda wa’adinsu ya ƙare, ba tare da karya doka ba.

DanAbdullo ya buƙaci Majalisa da ta yi amfani da ikon sa ido da take da shi, domin soke wannan dokar zartarwa.

Ya yi gargaɗi cewa idan ba a yi hakan ba, hakan na iya zama tushen matsala da zai lalata tsarin aikin gwamnati a Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Kano ma aikatan gwamnati an gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta

A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.

A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje