• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Masana’antar Kannywood: Ganin Kitse Ake Wa Rogo – Mai Sana’a

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
4 months ago
in Nishadi
0
Ci Gaban Masana’antar Kannywood: Ganin Kitse Ake Wa Rogo – Mai Sana’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Guda daga cikin manyan jarumai, masu shirya fina-finan barkwanci da fadakarwa, Musa Mai Sana’a, ya bayyana abin da ya sani dangane da ci gaban da ake tunanin Masana’antar Kannywood ta samu, inda ya ce; ko shakka babu ganin kitse ake yi wa rogo, idan ana yin maganar ci gaba a wannan masana’anta ta shirya fina-finan Hausa.

A wata hira da aka yi da Mai Sana’ar, a gidan rediyon muryar Amurka, ya bayyana batutuwa da dama da suka shafi rayuwa da sauran al’amura na yau da kullum, tunda farko dai; jarumin ya yi bayani a kan yadda wasu lokutan yake samo labarun wasu daga cikin fina-finansa, don nishadantarwa ko fadakar da masu kallo.

  • An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa
  • AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

“Wasu lokutan, nakan tashi na tafi wani waje, wanda idan na fada; ba lallai a yarda ba. Misali, idan na so nishadi ko na dan bukaci yawon shakatawa, nakan tafi wurare kamar wajen da masu sana’ar Adaidaita Sahu ke tsayawa; su dan huta bayan sun yi aiki sun gaji, da sauran wurare da za ka ga rayuwa iri-iri, wanda hakan zai iya ba ka dama ka kwaikwayi abubuwan da ka gani; ka mayar da shi shirin fim, domin mutane su amfana; su kuma karu da ilimin zaman duniya”, in ji shi.

Da yake amsa tambaya kan yadda yake samo wasu ayoyi da hadisan da yake yawan amfani da su a fina-finansa, sai ya ce; duk da shi ba Malamin Addini ba ne, amma kuma Almajiri ne da ya yi karatun addini bakin gwargwado. Ya kara da cewa, ba Darakta ba ne yake rubuta masa wadannan ayoyi ko hadisai da yake karantowa a fim ba, kawai dai yana fadar su ne daga abin da ya koya a gaban Malamansa na addini.

Mai Sana’a ya ci gaba da bayyana cewa, dangane da abin da mutane ke fada cewa, gwamnatin tarayya ta yi matukar taka rawar gani ko ta sallami Masana’antar Kannywood, a kan gudunmawar da suka bayar a lokacin yakin neman zabe ta hanyar nada wasu daga cikin manyan jarumai manyan mukaman gwamnati, ko kusa ba haka abin yake ba; domin kuwa ba masana’antar aka sallama ba, illa kawai daidaikun wasu daga cikinsu.

Labarai Masu Nasaba

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

Har ila yau ya ce, idan aka yi maganar mukaman da gwamnatin tarayya da ta jihohi suka bai wa wasu daga cikinmu, ba yana nufin cewa; an taimaki masana’antar ba ne, domin kuwa; mafi yawancin wadanda suka samu wadannan mukamai, babu wani ci gaba ko hobbasa da suka yi wajen ciyar da Masana’antar Kannywood gaba.

Musa ya ce, illa kawai dai suna taimakon kansu da kuma na kusa da su, wanda kuma ba haka ya dace a ce suna yi ba, dalili kuwa shi ne, har yau babu wani daga cikin masana’antar tamu da ya taba samun wani mukamin gwamnati, ya taimaka wa ita kanta masana’antar, illa kalilan daga cikinmu.

A bangaren abokanan fada kuwa a Masana’antar Kannywood, Mai Sana’a ya ce; duk da wannan magana da yake yi a halin yanzu, babu wani a masana’antar da zai bude baki ya ce; shi ne abokin fadansa, domin kuwa dukkanin wadanda suke tare a masana’antar, yana kallonsu da mutunci duk da cewa dai wasu sun fi wasu zama mutanen kirki.

A karshe, Musa ya bayyana cewa; idan Allah ya kawo wata sana’ar da ta fi wannan harka ta fim a wajensa, zai ajiye ta a cikin lumana; ba wai don ta yi masa tsaroro ba ba, kawai dai yana fatan wata rana wani abu daban zai zo, wanda ya fi masa harkar fim din, domin babu wani mutum a duniya da ba ya son cigaba, idan kuma wannan sana’a ita ce tsira a wajensa, yana fatan mutuwa a cikinta, ba tare da ya bar ta ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Fina-Finan Sin Ta Dire Matsayi Na Daya A Duniya Na Wucin Gadi A 2025

Next Post

Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

Related

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

23 hours ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

6 days ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

7 days ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

2 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

2 weeks ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

3 weeks ago
Next Post
Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

May 25, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

May 25, 2025
katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina

May 25, 2025
29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma

29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma

May 25, 2025
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

May 25, 2025
Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

May 25, 2025
Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

May 25, 2025
An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.