Zaftarewar ƙasa ta kashe mata masu haƙar zinare a Mali
Published: 31st, January 2025 GMT
Masu haƙar zinare aƙalla mutum 10 sun mutu wasu da dama sun ɓace bayan zaftarewar ƙasa a kansu a wani filin haƙar ma’adinai yankin Koulikokro na ƙasar Mali.
Hukumomin yankin sun bayyana cewa mata ne yawancin masu haƙar zinaren da abin ya rutsa da su mata ne, kuma an kasa ciro gawarwakinau, “saboda tsananin sarƙaƙiyar yanayin.
Gwamnatin yankin ya bayyana cewa ajali ya rutsa da su ne a ƙauyen Danga, a cikin wani rami mai ruwa da laka, wanda zaftarewar ƙasar ta binne su a ciki a ranar Laraba.
Ta bayyana a shafinta na Facebook cewa “abin takaicin shi ne babu ko mutum ɗaya da ya tsira a cikin su.”
Matashi ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai JigawaJami’in kula da haƙar ma’adanai a yankin, Ousmane Diakite, ya bayyana cewa, “akalla mutum 10 ne abin ya yi alajinsu.”
Wani jami’in gwamnati da ya nemi a bole sunansa ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa akwai yiwuwar adadin zai karu, a yayin da hukumomi ake ci gaba aikin ceto.
Magajin wani gari da ke maƙwabtaka da Koulikokro, ya bayyana wa AFP cewa, “babu wanda ya tsira bayan faruwar lamarin.”
Mali na daga cikin ƙasashe mafiya talauci a duniya, duk da cewa tana cikin ƙasashen mafiya arzikin zinare a nahiyar Afirka.
Zaftarewar ƙasa na yawan halaka masu haƙar zinare a ƙasar, a yayin da hukumomi ƙasar ko ƙoƙarin kawo ƙarshen amfani da hanyoyin gargajiya wajen gudanar da harkar.
A watan Janairun 2024 zaftarewar ƙasa ta kashe masu halartar zinare 70 a wurin da na ranar Larabar nan ya faru.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: haƙar zinare masu haƙar zinare
এছাড়াও পড়ুন:
ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
Ƙungiyar ISWAP mai yaƙi da tayar da ƙayar baya a yammacin Afirka, ta ɗauki alhakin harin da ya yi ajalin mutum 26 a Jihar Borno.
Ƙungiyar ta iƙirarin ɗaukar alhakin harin ne a wani saƙo da ta wallafa a shafin Telegram kamar yadda BBC ya ruwaito.
Aminiya ta ruwaito yadda wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalMajiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.
Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan ISWAP suka ɗana bam ɗin.
Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.
“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.
Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti.
Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.
An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.