Araghchi: Iran ba za ta tattauna kan batun inganta sinadarin Uranium din ta ba
Published: 22nd, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Iran ba za ta tattauna ba kan batun inganta sinadarin Uranium din ta a tattaunawar da ta ke da Amurka ba, kuma ba za ta yi watsi da wannan hakki ba a kowe irin dalili.
“A halin yanzu muna fuskantar wani matsayin Amurkawa marasa ma’ana wanda ya saba wa hankali.
Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada cewa Iran ta shiga tattaunawa don tabbatar da hakkokin al’ummar kasar, kuma ba za mu yi kasa a gwiwa ba a kan wadannan hakkokin.
“A ra’ayinmu, batun inganta [uranium] kwata-kwata ba abu ne da za a iya sasantawa ba,” in ji shi.
A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata na bayar da amsa karara, kuma a yau jagora ya fayyace matsayinmu, in ji Araghchi yayin da yake magana kan kalaman da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yi a ranar Talata, inda a cewarsa ba daidai ba ne Amurka ta dage cewa Iran ta daina ayyukanta na inganta makamashin Uranium ta hanyar lumana.
Ayatullah Khamenei ya ce: “hana Iran ta inganta sinadarin Uranium, babban kuskure ne.”
Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da manufofinta, hanyoyinta da kuma aiwatar da su, inji Jagoran inda ya jaddada cewa ba wani mahaluki da zai hana Iran inganta sinadarin urenium din ta.
A cikin ‘yan kwanakin nan, jami’an Amurka sun ce dole ne Iran ta kawo karshen duk wani aikin inganta sinadarin Uranium, batun da jami’an Iran suke ba zai yi wu ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Uranium
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Yana fatan tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshgan ya bayyana cewa: Iran tana fatan tattaunawarta da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya da za ta tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.
A yammacin jiya Lahadi, a gefen taron dandalin tattaunawa na Tehran na shekara ta 2025, a wata ganawa da ministan harkokin wajen masarautar Oman Badar bin Abdullah al-Busaidi, Shugaba Pezeshkian ya yaba da irin kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma irin rawar da gwamnatin Oman take takawa wajen daukar nauyin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Amurka da Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Yana mai cewa: “Suna fatan sakamakon kokari da kuma sahihan manufofin Sultan Haitham bin Tariq, wadannan shawarwarin za su kai ga cimma yarjejeniyar adalci da za ta tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.”
Shugaban na Iran ya jaddada wajabcin kara samun kusanci a tsakanin kasashen musulmi, yana mai cewa “masu kusanci da juna da fadada hadin gwiwarsu, haka nan masu fatan cutar da al’ummar musulmi za su zama masu haifar da sabani da rabuwar kai a tsakaninsu.”