Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Iran ba za ta tattauna ba kan batun inganta sinadarin Uranium din ta a tattaunawar da ta ke da Amurka ba, kuma ba za ta yi watsi da wannan hakki ba a kowe irin dalili.

“A halin yanzu muna fuskantar wani matsayin Amurkawa marasa ma’ana wanda ya saba wa hankali.

Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada cewa Iran ta shiga tattaunawa don tabbatar da hakkokin al’ummar kasar, kuma ba za mu yi kasa a gwiwa ba a kan wadannan hakkokin.

“A ra’ayinmu, batun inganta [uranium] kwata-kwata ba abu ne da za a iya sasantawa ba,” in ji shi.

A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata na bayar da amsa karara, kuma a yau jagora ya fayyace matsayinmu, in ji Araghchi yayin da yake magana kan kalaman da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yi a ranar Talata, inda a cewarsa ba daidai ba ne Amurka ta dage cewa Iran ta daina ayyukanta na inganta makamashin Uranium ta hanyar lumana.

Ayatullah Khamenei ya ce: “hana Iran ta inganta sinadarin Uranium, babban kuskure ne.”

Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da manufofinta, hanyoyinta da kuma aiwatar da su, inji Jagoran inda ya jaddada cewa ba wani mahaluki da zai hana Iran inganta sinadarin urenium din ta.

A cikin ‘yan kwanakin nan, jami’an Amurka sun ce dole ne Iran ta kawo karshen duk wani aikin inganta sinadarin Uranium, batun da jami’an Iran suke ba zai yi wu ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Uranium

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa

Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250  ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.

Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.

Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale  kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.

Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.

 

A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.

Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.

 

Abdullahi Jalaluddeen 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar