Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Iran ba za ta tattauna ba kan batun inganta sinadarin Uranium din ta a tattaunawar da ta ke da Amurka ba, kuma ba za ta yi watsi da wannan hakki ba a kowe irin dalili.

“A halin yanzu muna fuskantar wani matsayin Amurkawa marasa ma’ana wanda ya saba wa hankali.

Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada cewa Iran ta shiga tattaunawa don tabbatar da hakkokin al’ummar kasar, kuma ba za mu yi kasa a gwiwa ba a kan wadannan hakkokin.

“A ra’ayinmu, batun inganta [uranium] kwata-kwata ba abu ne da za a iya sasantawa ba,” in ji shi.

A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata na bayar da amsa karara, kuma a yau jagora ya fayyace matsayinmu, in ji Araghchi yayin da yake magana kan kalaman da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yi a ranar Talata, inda a cewarsa ba daidai ba ne Amurka ta dage cewa Iran ta daina ayyukanta na inganta makamashin Uranium ta hanyar lumana.

Ayatullah Khamenei ya ce: “hana Iran ta inganta sinadarin Uranium, babban kuskure ne.”

Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da manufofinta, hanyoyinta da kuma aiwatar da su, inji Jagoran inda ya jaddada cewa ba wani mahaluki da zai hana Iran inganta sinadarin urenium din ta.

A cikin ‘yan kwanakin nan, jami’an Amurka sun ce dole ne Iran ta kawo karshen duk wani aikin inganta sinadarin Uranium, batun da jami’an Iran suke ba zai yi wu ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Uranium

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

Aƙalla mutane takwas ne suka mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Atura Bus Stop, hanyar Lagos-Badagry, lokacin da wata motar haya ƙirar Mazda mai ɗaukar fasinjoji 16 ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota ƙirar DAF. Hukumar LASTMA ta bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a da rashin iya sarrafa mota daga direban motar hayar.

A cikin wata sanarwa, Daraktan Hulɗa da Jama’a na LASTMA, Adebayo Taofiq, ya ce hatsarin ya kasance mai muni matuƙa, inda ya kashe direban motar, yaran moto da sauran fasinjoji shida. Ya ce hatsarin ya jefa al’ummar yankin cikin alhini da ɗimuwa. Jami’an LASTMA, da FRSC, da rundunar ƴansanda da Sojoji daga Ibereko sun gudanar da aikin ceto cikin gaggawa.

Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau Jami’in LASTMA Na Bogi Da Ya Sato Mota Ya Shiga Hannu

An ceto mutane takwas da suka jikkata, kuma aka garzaya da su Asibitin Gwamnati da ke Badagry don samun kulawar gaggawa. Adebayo ya bayyana cewa hatsarin ya zama darasi, yana mai jaddada cewa gudu, da rashin kiyayewa da sakacin direbobi na ƙara haddasa irin waɗannan hatsarin a tituna.

Babban Manajan LASTMA, Olalekan Bakare-Oki, ya kai ziyara wurin da hatsarin ya faru, inda ya gargaɗi direbobi su kiyaye gudu da bin dokokin hanya. Ya ce gwamnati ta fara shigar da kayan rage gudu a wuraren da ke da haɗari domin rage yawaitar hatsura. Ya ƙara da cewa dole ne direbobi su nuna kishin ƙasa ta hanyar yin tuƙi cikin hankali da kiyaye lafiyar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis