Ma’aikatar yada labarai ta jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar kula da gidajen Radiyo da Talabijin ta kasa NBC sun shirya taron yini biyu ga masu fafutukar siyasa da masu sharhi kan harkokin yada labarai.

 

 

 

Taron na da nufin tsaftace harkar siyasa da inganta fahimtar juna tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

 

An zabo mahalarta taron ne daga jam’iyyun siyasa daban-daban da gidajen rediyo a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

 

A nasa jawabin, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ya bayyana cewa, a karshen taron, mahalarta taron za su fahimci ladubban da suka shafi harkokin siyasa.

 

Ya yi Allah wadai da karuwar kararrakin batanci da sunan siyasa, yana mai cewa masu fafutuka na siyasa, masu sharhi kan harkokin yada labarai da masu gabatar da shirye-shiryen siyasa na bukatar ilimin kan kyawawan ayyuka bisa al’adu da addini.

 

Kwamared Waiya ya nanata kudirin gwamnatin jihar na hada hannu da masu ruwa da tsaki domin ciyar da Kano gaba da kuma baiwa ‘yan kasa damar cin moriyar dimokradiyya.

 

“Ba mu zo nan don shawo kan kowa ya canza sheka zuwa wata jam’iyya ba amma don tsaftace tsarin”

 

Shima da yake nasa jawabin, kodinetan NBC na jihar Malam Adamu Salisu ya bayyana cewa taron bitar ya yi daidai da aikin hukumar, don haka akwai bukatar hada hannu da masu ruwa da tsaki domin cimma manufofin da ake bukata.

 

Ya yabawa ma’aikatar yada labarai kan wannan shiri, sannan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su bada gudunmawar ta hanyar samar da zaman lafiya.

 

Ya yi nuni da cewa taron ya yi daidai da aikin hukumar NBC.

 

Ko’odinetan jihar ya bayyana cewa masu fafutuka, masu sharhi kan harkokin yada labarai, da masu gabatar da shirye-shirye na da muhimmiyar rawa da za su taka a fagen siyasar Kano.

 

Da yake gabatar da kasida kan inganta magana mai kyau da kuma nisantar kalaman batanci a kafafen yada labarai ta mahangar Musulunci, babban limamin masallacin Al-furqan, Sheikh Bashir Aliyu Umar, ya bayyana wasu abubuwa guda uku na yada bayanai bisa koyarwar addinin Musulunci, wadanda suka hada da gaskiya, daidaito da kuma sanin yakamata.

 

Shugaban masu fafutukar siyasar jihar Kano, wanda aka fi sani da Gauta Club, Alhaji Hamius Danwawu Fagge, ya bayyana horon a matsayin wanda ya dace.

 

Ya yi alkawarin cewa mahalarta taron za su yi amfani da ilimin da aka samu wajen ci gaban Kano da Najeriya baki daya.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro yada labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.

Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.

Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.

Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.

Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.

Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa