Aminiya:
2025-04-30@19:33:09 GMT

Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe

Published: 24th, April 2025 GMT

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya  ba da umarnin gaggawa da a yi cikakken sauyi ga dabarun tsaron ƙasa, yana mai umartar shugabannin tsaro su ɗauki matakan gaggawa don daƙile ƙaruwar tashin hankali da kashe-kashe jihohin Borno, Filato, Binuwai, da Kwara.

Tinubu, wanda ya gana da shugabannin tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa, ya ce dole ne a kawo ƙarshen kashe-kashe a jihohin da abin ya shafa.

“Ya isa haka,” in ji Shugaba Tinubu yayin da ya sake yin tir da kai hari ga ’yan Najeriya ba tare da wani dalili ba.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa (NSA), Nuhu Ribadu, ya shaida wa manema labarai cewa shugabannin tsaron sun yi wa shugaban ƙasa cikakken bayani kan halin da tsaro ke ciki.

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa gidan rediyo na haɗin gwiwa NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Ribadu ya ce Shugaba Tinubu ya ba da umarnin amfani da sabbin dabaru don magance matsalolin rashin tsaro.

Ya ce, shugaban ƙasar “ya ba mu damar zuwa mu sake yi masa bayani. Ya ɗauki lokaci mai tsawo muna masa cikakken kan abin da ke faruwa.

“Ko da ya yi tafiya ƙasar waje yana yawan tuntuba, yana ba da umarni kuma yana bin diddigin abubuwan da ke faruwa. A yau kuma mun sami damar sake yi masa bayani na tsawon awanni.

“Mun saurara, kuma mun karɓi sabbin umarni daga gare shi. Gaskiya, ya nace cewa mu yi aiki tuƙuru don maido da tsaro a ƙasa.

“Mun yi masa bayani kan abin da ya faru kuma muka tabbatar masa da jajircewarmu.

“Mun aiwatar da umarninsa, mun je wuraren da ake fama da rashin tsaro, kamar jihohin Filato da Binuwai da Borno, kuma mun ba shi ra’ayinmu saboda ya ba mu umarni mu je mu gana da hukumomin siyasa a can,” in ji shi.

Ribadu ya ce Tinubu ya jaddada buƙatar ƙara shigar da ƙananan hukumomi da gwamnatocin jihohi wajen magance al’amuran rashin tsaro.

“Matsalar rashin tsaro sau da yawa ba ta tsaya ga manyan matakai kawai ba. Ta ƙunshi ƙananan hukumomi. Su ne ke tare da mutane kai tsaye, musamman ma idan wasu ƙalubalen sun shafi matsalolin al’umma.

“Muna buƙatar yin aiki da al’ummomi  da ƙananan hukumomi da kuma gwamnoni. Shugaban Ƙasa ya ba da umarni cewa mu ƙara yin aiki da gwamnoni,” in ji shi.

Ribadu ya ce Shugaban Ƙasa ya “damu sosai” a taron kuma ya ce “abin ya isa haka.”

Ribadu ya ce maharan galibi suna kai hari ne kan ’yan ƙasa marasa galihu ta hanyar dasa bama-bamai da kuma kai hari kan wuraren da ba su da gwamnati.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tsaro shugabannin tsaro Shugaban Ƙasa Ribadu ya ce rashin tsaro ba da umarni

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae

Kakakin ma’aikatar sharia a nan JMI ya bada sanarwan cewa,ma’aikatar za ta bayyanawa mutanen sakamakon bincken da suka gudanar kuma suke ci gaba da yi, dangane da fashewa da kuma gobatar da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Shahid Rajaee a cikin yan kwanakin da suka gabata. .

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran, ya bayyana cewa, Asgar Jahangir  kakakin ma’aikatar sharia da kuma Zabihullah Khudayiyan shugaban hukumar bincike ta kasa, sun gudanar da taron hadin guiwa da yan jaridu da kafafen yada labarai na cikin gida da waje a safiyar, dangane da fashewa da kuma gobarar da ta biyo baya a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajaee.

Banda haka jami’an sun amsa tambayoyin yan jarida bayan jawabansu dangane da hatsarin wanda ya lakume rayukan mutane, fiye da 70 da kuma jikata wasu kimani dubu guda.

Kafin haka dai jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaee ya bada umurni ga ma’aikatun biyu su gudanar da cikekken bincike don gani musabbabin wannan hatsarin sannan idan akwai wadanda suka da hannu, ko sakaci a cikinsa, a bi tsarin da ake da shi don hukunta wadanda suke da laifi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa