Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa” a yayin farmakin da ya kashe ma’aikatan jinya 15 a cikin watan Maris a zirin Gaza, wanda ya saba wa sakamakon wani rahoton bincike na cikin gida da sojojin Isra’ila suka fitar.

Wani jami’in tsaron farar hula a Gaza Mohammed al-Moughair ya shaidawa AFP cewa “Bidiyon da daya daga cikin ma’aikatan jinya ya dauka ya tabbatar da cewa rahoton da sojojin Isra’ila suka fitar akwai karairayi a ciki saboda ta aiwatar da hukuncin kisa.

Al-Moughair ya kuma zargi Isra’ila da neman kaucewa abinda ya wajaba kanta a karkashin dokokin kasa da kasa.

Tunda farko dama Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi watsi da rahoton da sojin Isra’ila suka fitar kan kisan da aka yi wa sama da jami’an agajin gaggawa na Gaza a watan da ya gabata, wanda gwamnatin kasar ta ce an kashe ne ta bisa kuskure.

Kungiyar ta yi fatali da rahoton na Isra’ila da cewa ba shi da inganci kuma ba za a amince da shi ba, tana mai jaddada cewa yana cike da karairayi.

A wani rahoto da suka fitar ka abinda ya faru sojojin Isra’ila sun yi ikirarin cewa, an samu ” kura-kurai da yawa” a kisan da akayi wa jami’an agajin a Gaza, suna masu cewa za a kori wani kwamandan sojoji.

“Binciken ya nuna cewa an samu wasu matsaloli na rashin da’a na kwararru, da rashin bin umarni, da kuma gaza yin cikakken bayani kan lamarin,” in ji rundunar.

A ranar 23 ga Maris, ne aka harbe wasu ma’aikatan agaji na Falasdinawa 15 da masu aikin ceto a kusa da Rafah da ke kudancin Gaza.

Kisan da akayi wa jami’an agajin gaggawa na falasdinu ya fuskanci tofin Allah-tsine daga kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.

Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.

Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki