HausaTv:
2025-06-15@16:36:50 GMT

A Kalla Falasdinawa 35 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24

Published: 21st, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; A kalla mutane 35 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 62 kuma su ka jikkata a cikin sa’o’i 24.

Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Gaza ta kara da cewa; Sojojin Mamaya sun kai wasu hare-hare a gabashin garin Beit-Hanun dake arewacin Gaza.

A cikin hemar ‘yan hijira dake tsakiyar Gaza, Falasdinawa 3 sun yi shahada, bayan da jiragen saman a ‘yan mamaya su ka kai hari.

A kudancin Gaza kuwa sojojin HKI sun tarwatsa wani gini na fararen hula a yankin Misbah dake arewacin birnin Rafah.

Daga ranar 18 ga watan Maris na wannan shekarar zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 1864, yayin da wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 4890.

Daga 7 ga watan Oktoba 2023 zuwa yanzu jumillar Falasdinawa da su ka yi shahada sun kai 51,240, sai kuma wani adadin da ya kai na mutane 116, 931, da su ka jikkata.

A gefe daya,kafafen watsa labarun HKI sun bayar da labarin cewa, wani yanayi mai tsanani ya faru a Gaza a yau Litinin,da hakan yake nufin cewa an kai wa sojojinsu hari mai tsanani wanda zai iya zama halaka wasu daga cikinsu.  Haka nan kuma kafafen watsa labarun na HKI sun ambaci cewa; Uku daga cikin sojojinta sun jikkata saboda fashewar wata nakiya da aka dasa a bakin hanya a Beit-Hanun dake arewacin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.

Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.

“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.

“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”

Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.

Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.

Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.

“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.

“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”

Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.

Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.

Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.

“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.

“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”

Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India