Karamin Ministan Tsaro a Najeriya Bello Matawalle, ya caccaki masu sukar lamirin Shugaban Kasa Bola Tinubu game da nuna wariya ga yankin Arewacin Najeriya.

Matawalle ya ce Tinubu kadara ne ga Arewa kuma ba shi da fatan da ya wuce ganin ya magance matsalolin da suka addabi yankin kafin 2027.

Cikin wani jawabi da mai taimaka masa kan sha’anin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fita, Matawalle ya ce ba a taba samun lokacin da ake yin dimokradiyya mai tsafta kamar a zamanin Bola Tinubu ba.

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

Ya ce duk masu kushe salon mulkinsa kawai suna huce haushin rashi ne da yada farfaganda da karairayi.

“Mutanen Arewa suna da wayewar da sun fi karfin a yaudare su domin cimma wata manufar siyasa. Akwai bukatar mu hada kai waje daya kada mu yarda a yaudare mu.” Inji Matawalle.

Ministan ya ce kamata ya yi a gode ma Tinubu saboda yadda yake inganta yankin Arewa da tsaro kuma ana ganin ci gaba musamman yankin da ya fito na Sokoto-Kebbi-Zamfara.

Bugu da kari ya yaba ma ayyukan ci gaban da yake kawo wa yankin musamman yadda ake shimfida tituna da kokarin kawo ci gaba ga yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bello Matawalle matawalle Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a a ‘Delta state’, na yi makarantar firamare da sakandare a Delta, sannan nayi aure a can. Yara na uku, Allah ya kawo rabuwa tsakani na da mijina. Babana dan ‘Nasarawa State’ ne, Mama ta kuma ‘yar Jihar Kano ce. Shekaruna Talatin da hudu, na tsinci kaina a masana’antar Kannywood ne shekara shida da suka wuce baya.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?

Saboda fim yana daya daga cikin abin da ya fara burge ni bayan aure na ya mutu, shi fim abu ne wanda yake kamar wa’azantarwa da kuma tunatarwa.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Yadda gwagwarmayar ya kasace shi ne; na zo fim ne ba tare da tunanin yadda za ta kasance da ni ba, amma yanzu kam Alhamdulillah.

 

Ya batun iyaye lokacin da za ki sanar musu kina sha’awar fara fim, shin kin samu wani kalubale daga gare su?

Eh, a gaskiya na samu. Saboda mahaifiya ta da ‘yan’uwana sun ki yarda, sai da na samu na zaunar da su na fahimtar da su sannan.

 

Da wane fim ki ka fara?

‘Motsin Rai’ wanda Yahaya Sa’id ne yayi daraktin, da kuma Dadin Kowa.

 

Ya farkon farawar ta kasance?

Gaskiya na sha wahala kasancewar shi ne farkon dasa min ‘camera’.

 

Da su wa ki ka fara cin karo a farkon shigarki kannywood?

Bosho, su Dan’Auta da sauransu.

 

Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

Gaskiya ba zan iya kirgawa ba.

 

Cikin finafinan da ki ka fito wanne ne ya zamo bakandamiyyarki?

Kishiyar uwa, saboda na fito a mahaukaciya abun dai abun armashi.

 

Wane irin nasarori ki ka samu game da fim?

Dalilin fim na je gurare wanda ban da ta wannan hanya, ban yi tunanin zuwa ba.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta cikin masana’antar?

Eh, kam ba za a rasa ba, to, amma Alhamdulillah.

 

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farinciki ko akasin haka, wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba a rayuwa?

Kamar mutuwar mahaifi na, ba zan taba iya mantawa ba har abada.

 

Ko kina da ubangida a masana’anyar Kannywood?

Eh, ina da shi.

 

Kafin shigarki masana’antar Kannywood wadanne jarumai ne suke burge ki, kuma me ya sa?

Ali nuhu, saboda yadda yake aikinsa kamar a gaske.

 

Mene ne burinki na gaba game da fim?

In zama babbar jaruma.

 

Bayan fim kina wata sana’ar ne?

Eh, ina ‘business’.

 

Misali wani daga cikin abokan aikinki ya ce yana sonki zai aure ki, shin za ki amince ki aure shi ko kuwa ba ki da ra’ayin auren dan fim?

Idan da so da kauna me zai hana.

 

Wasu na kokawa game da masana’antar kannywood, a takaice ya za ki yi wa masu karatu bayanin yadda masana’antar take, shin wace ce Kannywood ya cikinta yake?

Kannywood wata masana’anta ce wacce take kamar makaranta, kafin ka fara ta, dole sai ka mayar da hankali.

 

Wane kira za ki yi ga masu kokarin shiga kannywood?

Duk wacce za ta shigo ta dauka kamar koyan sana’a ce ya kawo ta, dole sai ta mayar da hankali tare da jajircewa.

 

Ko akwai wata shawara ko wani sako da ki ke da shi ga sauran abokan aikinki?

Sako na a gare su shi ne, su dinga rike gaskiya da amana, su sani mu kamar amana muke a hannunsu, su taya mu rike ta kima da mutuncin mu.

 

Me za ki ce da masoyanki masu kallon finafinanki?

Ina yi wa kowa fatan alkairi.

Muna godiya

Ni ma na gode.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales October 25, 2025 Nishadi Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad  October 11, 2025 Nishadi Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri? October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?