Karamin Ministan Tsaro a Najeriya Bello Matawalle, ya caccaki masu sukar lamirin Shugaban Kasa Bola Tinubu game da nuna wariya ga yankin Arewacin Najeriya.

Matawalle ya ce Tinubu kadara ne ga Arewa kuma ba shi da fatan da ya wuce ganin ya magance matsalolin da suka addabi yankin kafin 2027.

Cikin wani jawabi da mai taimaka masa kan sha’anin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fita, Matawalle ya ce ba a taba samun lokacin da ake yin dimokradiyya mai tsafta kamar a zamanin Bola Tinubu ba.

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

Ya ce duk masu kushe salon mulkinsa kawai suna huce haushin rashi ne da yada farfaganda da karairayi.

“Mutanen Arewa suna da wayewar da sun fi karfin a yaudare su domin cimma wata manufar siyasa. Akwai bukatar mu hada kai waje daya kada mu yarda a yaudare mu.” Inji Matawalle.

Ministan ya ce kamata ya yi a gode ma Tinubu saboda yadda yake inganta yankin Arewa da tsaro kuma ana ganin ci gaba musamman yankin da ya fito na Sokoto-Kebbi-Zamfara.

Bugu da kari ya yaba ma ayyukan ci gaban da yake kawo wa yankin musamman yadda ake shimfida tituna da kokarin kawo ci gaba ga yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bello Matawalle matawalle Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje

Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) Ola Olukoyede, ya mika katafaren jerin gidaje 750 na alfarma da aka kwace daga hannun tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ga Ministan Gidaje, Ahmed Musa Dangiwa. An mika takardun ne bayan wani takaitaccen taro da aka yi a Abuja, ranar Talata. Ministan ya ce, za a sayar da gidajen ne ta hanyar bayyanannen tsari da ya dace. “Za a yi amfani da ingantaccen tsari wajen sayar da gidajen ta hanyar shafin intanet na sabunta fata, da gwamnatin Tinubu ta kirkiro,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arsenal Na Dab Da Daukar Dan Wasan Gaba Viktor Gyokeres
  • Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 
  • EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku
  • Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?
  • Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)