Karamin Ministan Tsaro a Najeriya Bello Matawalle, ya caccaki masu sukar lamirin Shugaban Kasa Bola Tinubu game da nuna wariya ga yankin Arewacin Najeriya.

Matawalle ya ce Tinubu kadara ne ga Arewa kuma ba shi da fatan da ya wuce ganin ya magance matsalolin da suka addabi yankin kafin 2027.

Cikin wani jawabi da mai taimaka masa kan sha’anin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fita, Matawalle ya ce ba a taba samun lokacin da ake yin dimokradiyya mai tsafta kamar a zamanin Bola Tinubu ba.

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

Ya ce duk masu kushe salon mulkinsa kawai suna huce haushin rashi ne da yada farfaganda da karairayi.

“Mutanen Arewa suna da wayewar da sun fi karfin a yaudare su domin cimma wata manufar siyasa. Akwai bukatar mu hada kai waje daya kada mu yarda a yaudare mu.” Inji Matawalle.

Ministan ya ce kamata ya yi a gode ma Tinubu saboda yadda yake inganta yankin Arewa da tsaro kuma ana ganin ci gaba musamman yankin da ya fito na Sokoto-Kebbi-Zamfara.

Bugu da kari ya yaba ma ayyukan ci gaban da yake kawo wa yankin musamman yadda ake shimfida tituna da kokarin kawo ci gaba ga yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bello Matawalle matawalle Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

Ƙasar Iran ta bayyana shirinta na shiga tattaunawar sasantawa “idan aka tsagaita hare-hare”, kamar yadda ministan harkokin wajen ƙasar ya bayyana bayan ganawa da takwarorinsa daga Faransa, Burtaniya da Jamus.  

Yayin da ministocin Turai suka nuna sha’awar ci gaba da tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran, Shugaban Amurka Donald Trump ya nuna shakku kan yiwuwar nasara, yana mai cewa Iran tana son magana kai tsaye da Amurka.

Hakan ya faru ne a lokacin da rikici tsakanin Iran da Isra’ila ke ci gaba, inda Isra’ila ta kai hari kan wasu wurare a Tehran, kuma Iran ta mayar da martani da harin makamai.

Fadar White House ta bayyana cewa Trump zai yanke shawara cikin makonni biyu kan ko Amurka za ta ɗauki mataki kai tsaye a rikicin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
  • NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya
  • 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
  • Gamayyar Ƙungiyoyin Tinubu/Shettima Za Su Ƙaddamar Da Gangamin Yaƙi Da Masu Yi Wa Tafiyar Shetttima Zagon Ƙasa – Aminu Boyi 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje