Ban da wannan kuma, alkaluman PMI wato masu bayyana yanayin sayayya da ake ciki ta fuskar sana’o’in samar da kayayyaki a watan Maris ya samu karuwa cikin watanni 2 a jere, matakin da ya bayyana bukatun kasuwanni na kara samun kyautatuwa. Har ila yau, Sin ta kafa cikakken tsarin sana’o’i, da ingantattun manufofin dake da nasaba da su bayan kokarin da take yi a shekaru da dama, matakin da ya aza tubali mai inganci ga bunkasuwar tattalin arzikinta.

 

Bayan ga batun dorewa, Sin ta bayyana kuzarinta mai karfi a fannin samun bunkasuwa. A cikin shekarun baya-bayan nan, Sin ta sauya salon tattalin arzikinta daga matakin dogaro da zuba jari, da fitar da kaya waje, zuwa habaka bukatun cikin gida da gaggauta kirkire-kirkire tare. A shekaru 5 da suka gabata, bukatun cikin gida ya taka rawa da yawansa ya haura kashi 80 cikin dari ga bunkasuwar tattalin arzikinta. Alkaluman farkon watanni ukun bana, sun bayyana wannan sauyi da Sin take samu.

 

Yanayin bunkasuwar tattalin arzikin Sin mai karko da inganci a dogon lokaci ba zai canja ba duk da matsin lamba, da matakin karin harajin kwastam da Amurka ke kakabawa sauran sassa ke kawo mata a gajeren lokaci. Sin tana da kwarin gwiwa, da cikakken karfi tinkarar kalubaloli daga waje, da cimma muradunta na samun bunkasuwa bisa ingantattun manufofin gwamnatinta daga manyan fannoni. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Birnin Kano da Kewaye, Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi, ya bayyana ficewarsa a hukumance daga jam’iyyar NNPP.

Ƙoƙ8 inda ya danganta hakan da rikicin shugabanci da ke kara tsananta a cikin jam’iyyar.

PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu Abdulmumin Jibrin ya koma APC wata 2 bayan NNPP ta dakatar shi

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 11 ga Nuwamba, 2025, wacce aka aika wa Shugaban jam’iyyar a Unguwar Zaitawa a Karamar Hukumar ta Birni, Koki ya ce ya dauki wannan mataki ne bisa hakkin sa na kundin tsarin mulki na ’yancin shiga ko ficewa daga kowace jam’iyya.

“Bisa ga hakkin da kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa gyara) ya bani a sashe na 40, da kuma sashe na 7.1 na kundin tsarin mulkin NNPP da sauran dokoki, ina sanar da ficewata daga jam’iyyar NNPP daga ranar Talata, 11 ga Nuwamba, 2025,” in ji shi a cikin wasikar.

Ya bayyana cewa rikicin cikin gida da ya dabaibaye shugabancin jam’iyyar a matakin kasa ya sa shi a tsaka mai wuya, har ma ya zama kusan ba zai iya ci gaba da gudanar da aikinsa yadda ya kamata ba, da kuma samar da ingantaccen wakilci ga al’ummar mazaɓarsa a majalisar.

“Ficewa daga NNPP ya zama dole saboda rikicin shugabanci a matakin ƙasa ya sanya ba zan iya ci gaba da gudanar da aikina ba tare da kawo wakilci nagari ga mutanen Birnin Kano da Kewaye,” in ji shi.

Koki, wanda aka zabe shi a karkashin jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya nuna godiya ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi ya yi aiki, inda ya ce goyon baya da amincewar da ya samu daga ’ya’yan jam’iyyar sun kasance abin alfahari.

“Ina godiya matuka ga jam’iyyar bisa damar da ta bani na yi aiki a karkashinta. Goyon baya, amincewa da kwarewar da na samu a lokacin zama na dan jam’iyya sun kasance masu matukar muhimmanci, kuma ina godiya ga shugabanni da ’ya’yan jam’iyyar a dukkan matakai,” ya kara da cewa.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ɗan majalisar bai bayyana matakin siyasa na gaba ba ko jam’iyyar da zai shiga ba.

Dama dai tun a watannin baya an sha jin ’yan jam’iyyar ta NNPP na ɗaga masa yatsa saboda yadda suka ce ya cika yin mu’amala da ’yan jam’iyyar APC.

Matakin nasa kuma ma zuwa ne kwana biyu bayan takwaransa naazabar Kiru/Bebeji daga jihar, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya sanar da komawa APC watanni biyu bayan an kore daga NNPP.

Kazalika, kafin nan ma, jam’iyyar ta yi asarar Sanata da wasu ’yan majalisar tarayyar guda uku da su ma suka koma APC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
  • Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?
  • Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
  • Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu