Alkaluman Tattalin Arzikin Sin Sun Shaida Dorewar Ingancin Tattalin Arzikinta
Published: 18th, April 2025 GMT
Ban da wannan kuma, alkaluman PMI wato masu bayyana yanayin sayayya da ake ciki ta fuskar sana’o’in samar da kayayyaki a watan Maris ya samu karuwa cikin watanni 2 a jere, matakin da ya bayyana bukatun kasuwanni na kara samun kyautatuwa. Har ila yau, Sin ta kafa cikakken tsarin sana’o’i, da ingantattun manufofin dake da nasaba da su bayan kokarin da take yi a shekaru da dama, matakin da ya aza tubali mai inganci ga bunkasuwar tattalin arzikinta.
Bayan ga batun dorewa, Sin ta bayyana kuzarinta mai karfi a fannin samun bunkasuwa. A cikin shekarun baya-bayan nan, Sin ta sauya salon tattalin arzikinta daga matakin dogaro da zuba jari, da fitar da kaya waje, zuwa habaka bukatun cikin gida da gaggauta kirkire-kirkire tare. A shekaru 5 da suka gabata, bukatun cikin gida ya taka rawa da yawansa ya haura kashi 80 cikin dari ga bunkasuwar tattalin arzikinta. Alkaluman farkon watanni ukun bana, sun bayyana wannan sauyi da Sin take samu.
Yanayin bunkasuwar tattalin arzikin Sin mai karko da inganci a dogon lokaci ba zai canja ba duk da matsin lamba, da matakin karin harajin kwastam da Amurka ke kakabawa sauran sassa ke kawo mata a gajeren lokaci. Sin tana da kwarin gwiwa, da cikakken karfi tinkarar kalubaloli daga waje, da cimma muradunta na samun bunkasuwa bisa ingantattun manufofin gwamnatinta daga manyan fannoni. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
Daga Usman Muhammad Zaria
Ma’aikatar ilimi matakin farko ta jihar Jigawa ta ce za ta kashe fiye da naira miliyan dubu 18 domin gudanar da harkokinta a sabuwar shekara.
Kwamishinan ma’aikatar, Dr. Lawal Yunusa Danzomo ne ya bayyana haka lokacin da yake kare kiyasin kasafin kudin 2026 a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa.
Dr. Lawan Yunusa Danzomo ya ce zasu mayar da hankali ga aikin gina ajujuwa da gyaran wadanda suka lalace.
Za kuma a samar da littatafan darussa da tebura da kujeru domin inganta harkokin koyo da koyarwa.
Hakazalika za a gina bandakuna da samar da ruwan sha da wutar lantarki da tsaro.
Danzomo, ya ce aiwatar da haka zai yi matukar tabbatar da kyakkyawar da’irar ilimi da ta kunshi samar da ilimi cikin sauki ta hanyar shiga makaranta har a kammmala karatu.
Dr. Lawan Danzomo ya kara da cewar za a dauki malaman wucin gadi har su 4000 a karkashin shirin J-Teach.
Ya kuma yi nuni da cewar, za a shirya jarrabawa ga kason farko na malaman J-Teach su 1,450 na gwamnatin da ta gabata domin daukar su aiki na dindindin.
A nasa jawabin shugaban kwamatin ilimi matakin farkio na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Fagam, Alhaji Yahaya Zakari Kwarko ya bada tabbacin hadin kai da goyon baya domin samun nasarar da ake bukataa sabuwar shekara.