Ban da wannan kuma, alkaluman PMI wato masu bayyana yanayin sayayya da ake ciki ta fuskar sana’o’in samar da kayayyaki a watan Maris ya samu karuwa cikin watanni 2 a jere, matakin da ya bayyana bukatun kasuwanni na kara samun kyautatuwa. Har ila yau, Sin ta kafa cikakken tsarin sana’o’i, da ingantattun manufofin dake da nasaba da su bayan kokarin da take yi a shekaru da dama, matakin da ya aza tubali mai inganci ga bunkasuwar tattalin arzikinta.

 

Bayan ga batun dorewa, Sin ta bayyana kuzarinta mai karfi a fannin samun bunkasuwa. A cikin shekarun baya-bayan nan, Sin ta sauya salon tattalin arzikinta daga matakin dogaro da zuba jari, da fitar da kaya waje, zuwa habaka bukatun cikin gida da gaggauta kirkire-kirkire tare. A shekaru 5 da suka gabata, bukatun cikin gida ya taka rawa da yawansa ya haura kashi 80 cikin dari ga bunkasuwar tattalin arzikinta. Alkaluman farkon watanni ukun bana, sun bayyana wannan sauyi da Sin take samu.

 

Yanayin bunkasuwar tattalin arzikin Sin mai karko da inganci a dogon lokaci ba zai canja ba duk da matsin lamba, da matakin karin harajin kwastam da Amurka ke kakabawa sauran sassa ke kawo mata a gajeren lokaci. Sin tana da kwarin gwiwa, da cikakken karfi tinkarar kalubaloli daga waje, da cimma muradunta na samun bunkasuwa bisa ingantattun manufofin gwamnatinta daga manyan fannoni. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin domin tabbatar da dimokuradiyya a kasar.

Majalisar ta kuma ce tana goyon bayan matakin da shugaban ya ɗauka kwanaki kafin haka domin hana yunƙurin kifar da tsarin dimokuraɗiyya a makwabciyar kasar.

Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Bukatar dai na kunshe ne a cikin wata wasiƙa da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zamanta.

Tinubu ya umarci tura sojojin makon da ya gabata domin dakile yunƙurin karɓar mulki ba bisa ka’ida ba a Jamhuriyar Benin da kuma kaucewa rikicewar tsaro a yankin yammacin Afirka.

Sai dai Tinubu bai nemi amincewar majalisa ba kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Bayan karanta wasiƙar, majalisar ta koma zaman kwamiti domin tantance bukatar. A yayin zaman, ’yan majalisa sun tattauna kan tasirin tsaro, jin‑ƙai da diflomasiyya da ke tattare da wannan mataki.

Babbar damuwar a cewarsu ta haɗa da yiwuwar kwararar ’yan gudun hijira zuwa Najeriya, tsaron iyaka da kuma tasirin matakin ga zaman lafiya da tsaro a yankin.

Bayan doguwar muhawara, majalisar ta koma zama a zaurenta, inda ta kada kuri’ar amincewa da matakin shugaban ƙasa cikin rinjaye.

Shugaban Majalisar, Akpabio, ya gabatar da rahoton kwamitin domin tabbatarwa, inda ’yan majalisa suka amince ba tare da wata adawa ba kafin su amince da tura sojojin ta hanyar kada kuri’ar murya karo na biyu.

A jawabin sa, Akpabio ya yabawa Shugaba Tinubu bisa ɗaukar matakan da suka tabbatar da zaman lafiya a yankin da kuma bin ka’idojin kundin tsarin mulki ta hanyar neman amincewar majalisa, ko da bayan tura sojojin cikin gaggawa.

“Wannan mataki ne da ya zama dole. Shugaban Ƙasa ya yi aiki ne domin kare tsaron ƙasa da kuma kare dimokuraɗiyya a yammacin Afirka. Barazana ga kasa ɗaya barazana ce ga kowa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za a isar da kudurin majalisar ga Shugaban Ƙasa nan take.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda