Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-18@12:14:31 GMT

Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya

Published: 15th, April 2025 GMT

Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen daukar nauyin dalibai 70 zuwa Masarautar Saudiyya domin karatun digiri a fannoni na addini da na zamani.

Wannan na daga cikin shirin Kaura Capacity Building Project 2025 karkashin ma’aikatar kula da harkokin addinai ta jihar.

A yayin wani taron manema labarai, mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin addinali, Injiniya Imran bn Usman, ya bayyana cewa kowanne daga cikin kananan hukumomi 20 na jihar za su ba da sunayen dalibai uku, yayin da aka ware wa babban birnin jihar, Birnin Kebbi, guraben dalibai 10.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ce za ta dauki nauyin tafiyar daliban zuwa Saudiyya, yayin da gwamnatin Saudiyya za ta dauki nauyin karatunsu da walwalarsu bayan isarsu.

Mai ba da shawarar ya kara da cewa, ana sa ran kowacce karamar hukuma za ta gabatar da dalibai maza biyu da mace daya, don neman guraben karatun digiri a fannin addinin Musulunci ko sauran fannoni na zamani.

Ya kuma kara da cewa, an kammala shirin tura limaman masallatai Jumu’a zuwa kasashen waje domin horo na gajeren lokaci a fannin yadda ake gabatar da huduba da Hadisi, don kara inganta tasirinsu yayin gabatarda Sallah.

 

Daga Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Har yanzu ba a saka ranar sauraron ƙarar ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nazari Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna? November 16, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7 November 15, 2025 Manyan Labarai Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
  • ’Yan ta’adda sun yi garkuwa da dalibai 25 a Kebbi
  • Nukiliya : Iran zata sake duba huldarta da IAEA idan aka dauki wani sabon mataki kanta
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
  • Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
  • Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji