Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
Published: 8th, April 2025 GMT
Hukumar Kula da Jin DDaɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta ayyana ranar Juma’a 11 ga Afirilun 2025 a matsayin ranar ƙarshe da za a kammala biyan kuɗin aikin hajjin bana ga dukkan maniyyatan jihar.
Shugaban hukumar, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana hakan a yayin wata hira da manema labarai a Ilori.
Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa jimillar kuɗin aikin hajjin bana ya kai naira miliyan 8,459,000.
Ya yi kira ga dukkan maniyyatan da suka fara biyan kuɗi da su tabbatar sun kammala ragowar kuɗin kafin ranar ƙarshe, wato 11 ga Afrilu, domin ba za a ƙara lokaci ba.
Alhaji Abdulsalam ya kuma buƙaci maniyyatan da su gaggauta miƙa fasfo ɗin su na tafiya ƙasashen waje ga jami’ansu domin fara aikin biza ba tare da wani jinkiri ba, yana mai jaddada cewa fasfo mai inganci da ke da aƙalla watanni shida da fara amfani ne kawai za a amince da shi.
Ya bayyana cewa miƙa fasfo da wuri na da matuƙar muhimmanci domin kauce wa jinkiri ko rikice-rikicen da ka iya tasowa wajen fitar da biza a ƙarshe.
Alhaji Abdulsalam ya shawarci maniyyatan da su kasance masu ɗabi’a tagari da yayin zamansu a kasa mai tsarki.
Ya bayyana cewa kamfanin jirgin sama na Max Air ne aka bai wa alhakin jigilar mahajjatan Jihar Kwara na shekarar 2025 hukumance, yana mai cewa hukumar alhazan na aiki kafada da kafada da kamfanin don tabbatar da tafiyar da aikin jigilar cikin kwanciyar hankali kuma akan lokaci.
Ali Muhammad Rabi’u
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
A cewarsa, binciken da ake yi ya nuna cewa, shawarar da aka yanke na fara gudanar da aikin matatar man ta Fatakwal kafin a kammala cikakken aikin gyaranta bai kamata ba.
Ya kara da cewa, duk da cewa an kokarta kan farfado da dukkan matatun man guda uku. Sai dai da dama na kira ga cewa, ya kamata a yi hadin gwiwa a fannin fasaha don kammala aikin gyaran matatar mai ta Fatakwal, amma sayar da ita, zai kara ruguza darajarta.
Wannan tsakaci ya zo ne biyo bayan rade-radin da ake ta yadawa bayan kalaman shugaban NNPC, Ojulari a taron OPEC na shekarar 2025 da aka yi a Vienna na kasar Ostiriya a farkon wannan watan, inda ya yi nuni da cewa “komai na iya faruwa da matatar” yayin wata hira da Bloomberg.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp