Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi
Published: 30th, March 2025 GMT
Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su guji cin mutuncin shugabanni yayin da suke bayyana matsalolinsu, inda ya jaddada cewa girmamawa da ladabi suna fi tasiri wajen samun mafita.
“Idan ka zagi shugabanka, ta yaya kake so ya taimaka maka?” in ji shi.
Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah“Amma idan ka yi magana da ladabi, zai saurare ka kuma ya ɗauki mataki.
Da yake jawabi bayan sallar Idi a Sakkwato, Sarkin Musulmi, ya buƙaci ’yan Najeriya da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’a da kuma zaman lafiya da ci gaban ƙasa.
“Ku yi wa Shugaban Ƙasa, Gwamnoni da sauran shugabanni addu’a domin Allah Ya ba su ikon sauke nauyin da ke kansu,” in ji shi.
Ya taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan tare da yin kira da su ci gaba da koyi da halaye nagari da suka koya a cikin wata mai alfarma.
Hakazalika, ya jinjina wa malamai kan yadda suka gudanar da wa’azin Ramadan cikin hikima, tare da buƙatar su ci gaba da yaɗa zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: girmamawa Sarkin Musulmi Talakawa
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.
Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.
Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.
Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.
Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.
Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.
Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.
Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata, wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.
Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.
Daga Abdullahi Tukur