‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
Published: 30th, March 2025 GMT
A jiya Asabar dubun dubatar ‘yan hamayyar siyasa su ka yi gangami a birnin Stanbul bayan da jam’iyyar “National Party” ta gayyace su, domin ci gaba da yin tir da kamun da aka yi wa Akram Imam Uglu wanda shi ne magajin garin na Stanbul.
Shugagan jam’iyyar “Turkish National Party’ ta adawa, Uzgur Ozil ya bayyana cewa adadin wadanda su ka halarci gangamin sun kai miliyan 2.
Daga cikin mahalarta gangamin da akwai mata da mahaifan Akram Ima wadanda su ka rika bayar da taken cewa za a ci gaba da yin gwgawarmaya ako’ina.”
Tun da asubahin jiya Asabar ne dai mutane su ka fara yin tururuwa a cikin birnin na birnin Sitanbul suna dauke da tutocin turkiya da kuma hotunan Mustafa Kamal Ataturk wanda ya kafa jamhuriyar Turkiya.
Tun bayan da aka kama Imam Uglu a ranar 19 ga watan Maris ne dai kasar ta Turkiya ta fada cikin dambaruwar siyasar wacce an dade ba a ga irinta ba.
Shugaban jam’iyyar hamayyar ya fadawa jaridar “ Lo Monde” ta Faransa cewa a kowace Asabar za su zabi garin da za su gudanar da Zanga-zanga,sannan kuma da kowane marecen Laraba a cikin birnin Sitanbul.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar
Mamban a majalisar koli ta siyasar kasar Yemen ya aika sako ga mahalarta taron birnin Doha fadar mulkin kasar Qatar
Mohammed Ali al-Houthi, mamba a majalisar koli ta siyasar kasar Yemen, ya aike da sako ga shugabannin kasashen Larabawa da na kasashen musulmi da suka hallara a yau, Litinin, a taron Doha. Wannan taron na zuwa ne biyo bayan ha’incin yahudawan sahayoniyya da suka yi yunkurin halaka tawagar Hamas a babban birnin kasar Qatar.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, al-Houthi ya ce: “Sakonsa ga taron da za a yi a yau Litinin a birnin Doha na kasar Qatar, shi ne cewa: Matsayi mafi karfi shi ne tabbatar da halaccin jihadi da ‘yan mamaya da goyon bayan gwagwarmaya da kuma ayyana Isra’ila a matsayar ‘yar ta’adda.”
Ya kara da cewa: “Wannan zai kawo karshen rikici tare da dakatar da tashe-tashen hankula da wuce gona da iri.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci