Wannan ya sa murnar da wasu ke yi ta komawa da haska finafinan Hausa masu dogon zango a tashar YouTube ta fara komawa ciki.

Me ya sa ba a gamawa din?

BBC Hausa ta ci gaba da cewa wani faifan bidiyo na wata tattaunawa da jagoran shirin Izzar so, Ahmad Lawan ya yi a tasharsa ta Bakori TV, ya ce masu kallo ne ba su gaji da kallon shirin ba, shi ya sa ba zai daina ba.

Ya ce kasancewar Youtube ya dade kudu, amma bai je arewacin Nijeriya ba ne ya sa su ka gwada domin su koya wa mutanen arewa kallon fim a YouTube, shi kuma wannan fim din ya na ciki, ko in ce shi ne daya tilo da ya koya wa mutane kallo a YouTube, kuma mutane ba su gaji da kallonsa ba,” in ji shi, inda ya kara da cewa, “ka ga babu dalilin da zai sa mu daina.”

Na biyu kuma shi ne akwai abubuwa na addini da muke kawowa da suke tasiri a zukatan al’umma kamar soyayyar Annabi SAW, sannan akwai abubuwa da dama da an manta su a cikin addini, idan muka nuna sai su zama matashiya, fitaccen jarumin ya kara da cewa a sanadiyar dim din akwai akalla mutum uku da suka karvi addinin musulunci, wanda a cewarsa hakan na cikin abubuwan da suka sa bai daina fim din ba.

Hakazalika fitaccen marubuci kuma furodusa, Nazir Adam Salihi, wanda yake cikin marubuta shirin dadin kowa mai dogon zango, kuma forudusan shirin Gidan Badamasi, ya ce nan gaba kadan za a fara kammala wasu shirye-shirye.

Ya ce “mu ne muka fara fina-finan nan masu dogon zango, kuma sama da shekara 10 ne da suke wuce ne muka fara zuwa yanzu, a Turai irin su Ingila kuma akwai finafinai masu dogon zango da aka yi shekara 65 ana yi ba a gama ba, ka ga ba za a yi gaggawar cewa ba a gama na Hausa mu da muka fara sama da shekara 10 da suka wuce.”

Sai dai ya ce akwai wasu fina-finai da aka gama daukarsu, “nan gaba kadan zuwa shekara mai zuwa za a kammala wasu fina-finan, a shiga wasu daban, a game da ko ana karancin labaran ne, marubucin ya ce Hausawa na da labarai masu kyau da inganci.

A karshe Salihi ya ba marubuta shawarar su dage da karatu da bincike da kuma natsuwa wajen rubuta labaransu, da yake jawabi kan lamarin, dokta Muhsin Ibrahim, malami a Jami’ar Cologne da ke Jamus ya ce wannan matsala ce ga masana’antar, wadda ba za ta haifa da mai ido ba.

A cewarsa, abin da yake faruwa shi ne masu shirya fina-finan su na fargabar idan suka daina fim din ba dole ba ne wanda za su fara din ya samu karvuwa kamar shi, sai dai ya ce wannan matsala ce babba saboda “babu labarin da ba shi da karshe kuma duk hakurin mai kallo ana iya kure shi.”

Ya ci gaba da cewa duk masana’antun fim na duniya da suka ci gaba a duk labarin da suka tsara, akwai farkonsa da tsakiya da karshe, shi ya sa nake ganin wannan rashin dabara ce saboda yan kallon da suke tunani dai dole sai sun kubuce musu, musamman idan sun samu wani fim da ya fi wannan.

Muhsin ya kara da cewa ya kamata a ce duk wani fim da za a fara, a san cewa za a iya fara wani wanda ya fi shi ko kuma ya gaza shi, misali shirin Labarina mai dogon zango, duk da cewa Aminu Saira ya rike sunan, ai na biyu ya fi na farko karvuwa, shi fim din kamfanin Uk Entertainment ai Garwashi ya fi Fatake karvuwa,” in ji shi.

Ya ce rashin gama fim yana rage wa masu kallo karsashin ci gaba da kallon saboda fargabar ko sun fara kallo, suna tunanin ba za a gama ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu