HausaTv:
2025-07-06@20:48:23 GMT

Zelensky ya je Saudiyya domin tattaunawar zaman lafiya

Published: 11th, March 2025 GMT

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya isa kasar Saudiyya domin ganawa da yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman, gabanin wata muhimmiyar ganawa tsakanin tawagogin Ukraine da na Amurka domin share fagen shawarwarin zaman lafiya da Rasha a nan gaba.

Taron dai na nuni da wani gagarumin yunkurin diflomasiyya na magance rikicin da ke faruwa a Ukraine kuma zai iya ba da damar tsagaita bude wuta a cewar rahotanni.

Tattaunawar da za a yi a Jeddah ita ce ganawa ta farko tsakanin jami’an Ukraine da Amurka tun bayan ziyarar da Zelensky ya kai fadar White House a karshen watan Fabrairu da ya gabata, wanda ya haifar da cacar baki baki mai zafi tsakaninsa da shugaban Amurka Donald Trump.

Tun bayan hakan ne, gwamnatin Washington ta dakatar da taimakon soji ga Ukraine, lamarin da ya sa Kyiv ta nemi sulhu.

Zelenskyy ya bayyana cewa, “Muna fatan tattaunawa tare da amincewa kan shawarwari da ayyukan da suka dace,” yana mai jaddada cewa Ukraine na goyon bayan tattaunawa mai ma’ana tare da son a yi la’akari da muradunta.

Taron na ranar Talata zai mayar da hankali ne kan kafa tsarin zaman lafiya da tsagaita bude wuta tsakanin Rasha da Ukraine.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta sanar da cewa: Ta gabatar da martani mai kyau ga shawarar dakatar da bude wuta tsakaninta da gwamnatin mamayar Isra’ila

Kungiyar Hamas ta sanar da kammala tuntubarta tare da gabatar da kyakkyawar amsa ga sabuwar shawarar neman dakatar da bude wuta, inda ta bayyana shirinta na nan take na yin shawarwari kan tsarin aiwatarwa.

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci a Falastinu ta Hamas ta sanar a yammacin jiya Juma’a cewa ta kammala shawarwarin cikin gida da kuma tuntubar wasu bangarori da dakarun Falasdinawa dangane da sabuwar shawara da masu shiga tsakani suka gabatar na dakatar da hare-haren wuce gona da iri kan al’ummar Falasdinu a zirin Gaza.

Kungiyar ta yi nuni da cewa ta mika martanin ta ga ‘yan uwanta da ke shiga tsakani, inda ta tabbatar da cewa martanin yana da kyau. Ta sake nanata cewa a shirye take ta gaggauta shiga wani zagaye na tattaunawa kan hanyoyin aiwatar da wannan tsarin.

A cikin wannan mahallin, kafofin watsa labaru na haramtacciyar kasar Isra’ila sun ba da rahoton cewa, an sami wasu muhimman sauye-sauye a daftarin na Witkoff, wanda dukkansu ke goyon bayan Hamas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Ta Amince Da Tattaunawa Don Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
  • An Bude Mafiya Yawan Tashoshin Jiragen Sama A Iran Bayan Tsaida Yaki