Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Ga Tattaunawar Amurka Da Rasha Kan Rikicin Ukraine
Published: 19th, February 2025 GMT
Kasar Sin na maraba da duk kokarin da ake yi cikin lumana don warware rikicin kasar Ukraine, ciki har da tattaunawa tsakanin Amurka da Rasha, kuma Sin na fatan dukkan bangarori da masu ruwa da tsaki za su shiga cikin shawarwarin samar da zaman lafiya in lokaci yayi.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ne ya bayyana hakan a taron manema labarai na yau Talata, yana mai cewa, ko da yaushe kasar Sin tana da yakinin cewa, tattaunawa da yin shawarwari, ita ce hanya daya tilo da za a iya warware rikicin, kuma ta himmatu wajen inganta shawarwari don samar da zaman lafiya.
Ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga wata tambaya game da ganawar da jami’an Amurka da na Rasha suka yi a ranar Talata a birnin Riyadh na kasar Saudiyya, ba tare da halartar Ukraine ba. (Mohammed Yahaya)
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
Wani jami’in kasar Ukiraniya ya bayyana cewa, a kalla mutane 8 ne su ka jikkata sanadiyyar munanan hare-haren da Rasha ta kai wa birnin Kiev ta hanyar amfani da makamai masu linzami.
Shugaban sha’anin tafiyar da Mulki na soja a birnin Kiev Taimur Tikatishinko ya wallafa sanarwa a shafinsa na “Telegram’ cewa; A tsakanin wadanda su ka jikkata din da akwai karamin yaro dan shekaru 3, kuma tuni an dauki mutane 4 zuwa asibiti, daya daga cikinsu yana cikin mummunan hali.
Shi kuwa magajin birnin na Kiev Fitali Kikitshiko cewa ya yi, mutanen da su ka jikkata suna zaune ne a cikin gidaje mabanbanta a unguwa daya.
Har ila yau ya kara da cea; Harin ya haddasa fashewa mai karfi wacce ta sa tagogin gidaje su ka fashe, har zuwa gine-gine masu hawa 11.
A wani labarin daga jami’an kasar ta Ukiraniya, Rasha ta kai wasu hare-haren da jirage marasa matuki a garin Kirofifitsky wanda ya haddasa fashewa mai yawa.
A cikin makwannin bayan nan dai Rasha ta tsananta kai hare-hare a fadin kasar Ukiraniya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuki.
Tun a 2022 ne dai Rasha ta fara kai wa Ukiraniya hare-hare bisa dalilin cewa tana son shiga cikin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato.
Kasar ta Ukiraniya dai tana samun taimakon makamai da bayanai na sirri daga kungiyar ta Nato.