Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Irin Gagarumar Rawar Da Iran Ta Taka A Fegen Tsaro Yakin Tekun Pasha
Published: 18th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Iran tana taka rawa ta musamman wajen wanzar da kwanciyar hankali da tsaron yankin Tekun Pasha
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta hanyar mallakar mafi yawan layukan kan iyaka da tekun Pasha da kuma iko da mashigar Hormuz, ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali da tsaron wannan ruwa da yankunan makwabtanta.
Abbas Araqchi ya bayyana hakan ne a yayin taron tarihin huldar kasashen waje na Iran karo na 8, mai taken “Manufar harkokin wajen Iran da gabar tekun Pasha a cikin mahallin tarihi,” wanda aka gudanar a safiyar yau Talata a cibiyar nazarin siyasa da kasa da kasa na ma’aikatar harkokin wajen kasar: Tun daga tsawon tarihi har zuwa yanzu, yankin Tekun Pasha, yana matsayin daya daga cikin muhimman bangarorin ruwa a duniya, kuma yana daya daga cikin muhimman yankuna da suka shafi ci gaban rayuwar bil’adama, da muhimman tsare-tsare a fuskar mahanga daban-daban na bangarorin rayuwar dan Adam, wannan yanki na tekun Pasha yana nan a tunanin bil-Adama kuma ya cancanci matsayi da kulawa da bincike daga bangarori daban-daban.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.
Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.
Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.
‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’
Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.
Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.
Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp