Aminiya:
2025-11-02@14:16:44 GMT

Za a koma rubuta jarabawar WAEC a komfuta

Published: 4th, September 2025 GMT

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana goyon bayanta kan shirin mayar da rubuta Jarabawar Kammala Sakandare ta Yammacin Afirka (WAEC) da komfuta wato CBT daga shekarar 2026.

Wannan babban sauyin, wanda aka tsara cewa zai fara aiki a shekarar 2026 ya jawo mabambantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin ilimi.

An kama wata uwa kan binne jaririyarta a Kebbi Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja

Da yake jawabi a gaban Majalisar Dokoki da manyan masu ruwa da tsaki a wani taron wayar da kai a Abuja, Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya ce jarabawa ta tsarin CBT da za a dinga yi a duk faɗin ƙasar, zai ƙarfafa tsarin ilimin ƙasar.

Alausa ya ce Gwamnatin Tarayya tana goyon bayan rubuta jarabawar WAEC ta komfuta saboda a kawar da satar amsa da kuma tabbatar da an yi sahihiyar jarabawa.

“Mun ɗau aniyar mayar da rubuta jarabawa ta tsarin fasahar komfuta a matsayin wani mataki na samar wa fannin ilimi martaba.

“An yi wannan tsari na rubuta jarabawa ta komfuta saboda a rage satar amsa da kare martabar jarabawowinmu. Hakan zai ƙarfafa darajar jarabawowinmu a cikin gida da ma ƙasashen waje.

Ministan ya ƙara da cewa, duk da cewa wasu sun nuna adawa a farko, amma gwamnati tana ganin ya wajaba a dakatar da dogato tsohon tsarin da aka saba na takarda da biro.

A nasa bangaren, Shugaban Ofishin WAEC na Ƙasa, Amos Dangut ya ce an samu nasara a wannan sabon sauyin wanda aka fara gwajinsa a kan ɗalibai masu rubuta jarabawar WAEC ta kuɗi mai zaman kanta a shekarar 2024, kuma za a ƙara bunƙasa shi a faɗin kasar.

Dangut ya bayyana cewa, za a ɓullo da tsarin yin gwaji da koya wa ɗalibai yadda tsarin yake don taimaka musu wajen fahimtarsa sosai, yana mai jaddada cewa babu wani dalibi da za a bari baya.

Dangane da abubuwan da suka shafi samar da kayan aiki da matsalolin intanet, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa WAEC ta yi nasarar gudanar da jarabawar a wuraren da ke da wahalar isa ba tare da an samu cikas ba.

Ya ƙara da cewa zuwa yanzu sakamakon ɗaliban da suka rubuta jarabawar gwajin ta komfuta ya yi kyau sosai fiye da jarabawar takarda da aka saba rubutawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jarabawa WAEC rubuta jarabawar rubuta jarabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC