Na bar APC saboda Tinubu bai cika alƙawarin da ya yi ba — Marafa
Published: 29th, August 2025 GMT
Sanata Kabiru Garba Marafa tsohon ɗan Majalisar Dattawa da ya wakilci yankin Zamfara ta tsakiya jigo a Jam’iyar APC a jihar ya fice daga jam’iyar.
Sanata Marafa ya bayyana ficewarsa a wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook a ranar Jumu’a ya ce bayan tattaunawa da magoya bayansa sun cimma matsayar barin Jam’iyyar APC kan ta zalunce su.
“Bayan mun yi waiwaye a shekara biyu da rabi da suka gabata mun gano cewa, APC a matakin ƙasa da jiha ta zalunce mu, a matakin jiha lalacewar jam’iyar ya kai matuƙa tun bayan kafa kwamitin riƙon ƙwarya har zuwa yanzu ba a taɓa zama ko na minti biyar ba, don tattauna halin jam’iya, kuma ita ce ta fasa jam’iya gidan wane da gidan wane a haka ake tafiya.
“Shekara biyu da rabi ba a ɗunke baraka ba, don haka mun barwa ɓangaren Sanata Abdul’aziz Yari da Minista Bello Matawalle jam’iyar.
“Matsalar tsaro da ke addabar jihar na cikin abin da ya sa muka yi zama don duba halin da ake ciki, yanda APC ta yi na tilas sai ta yi nasara a zaɓen Ɗan Majalisa na Ƙaura da aka yi baya cikin alƙawarin da aka yi mana, shugaban ƙasa ya yi mana alƙawalin zai duba lamarin tsaro na Jihar Zamfara, hakan ya sa ya ɗauki jihohi biyu da ya ci zaɓe, ya ba su ministocin tsaro, a Zamfara ba abin da aka yi mana.”
Kan kalaman da ake yi sun bar APC ne don ba a ba su muƙami ba ne? Ya ce haka ne, ai suna siyasa ne don su samu muƙami su amfanar da al’ummarsu, “don me wani zai tsaya takara mu yi kamfe a zaɓe shi a ƙarshe ya ce shi ba abin da zai ba mu, wannan ba adalci ba ne don haka mun jingine Jam’iyar APC.
“A nan gaba za mu sanar da jam’iyyar da muka koma, sai a yi yaƙin gaba da gaba kana can ina nan,” kalaman Kabiru Marafa.
Sakataren yaɗa labarai na Jami’iyar APC a Zamfara Yusuf Idris, ya ce ba za su ce komai ba kan kalaman Sanata Kabiru Marafa domin bai rubuta masu ya sanar da su ya bar APC ba tun daga kan mazaɓarsa har zuwa matakin jiha.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bello Matawalle Sanata Kabiru Marafa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA