Aminiya:
2025-11-02@12:27:43 GMT

Na bar APC saboda Tinubu bai cika alƙawarin da ya yi ba — Marafa

Published: 29th, August 2025 GMT

Sanata Kabiru Garba Marafa tsohon ɗan Majalisar Dattawa da ya wakilci yankin Zamfara ta tsakiya jigo a Jam’iyar APC a jihar ya fice daga jam’iyar.

Sanata Marafa ya bayyana ficewarsa a wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook a ranar Jumu’a ya ce bayan tattaunawa da magoya bayansa sun cimma matsayar barin Jam’iyyar APC kan ta zalunce su.

An kama wani mutum da laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita Ƙara Kuɗin Fasfo: Gwamnati na jefa ’yan Najeriya cikin matsi — Obi

“Bayan mun yi waiwaye a shekara biyu da rabi da suka gabata mun gano cewa, APC a matakin ƙasa da jiha ta zalunce mu, a matakin jiha lalacewar jam’iyar ya kai matuƙa tun bayan kafa kwamitin riƙon ƙwarya har zuwa yanzu ba a taɓa zama ko na minti biyar ba, don tattauna halin jam’iya, kuma ita ce ta fasa jam’iya gidan wane da gidan wane a haka ake tafiya.

“Shekara biyu da rabi ba a ɗunke baraka ba, don haka mun barwa ɓangaren Sanata Abdul’aziz Yari da Minista Bello Matawalle jam’iyar.

“Matsalar tsaro da ke addabar jihar na cikin abin da ya sa muka yi zama don duba halin da ake ciki, yanda APC ta yi na tilas sai ta yi nasara a zaɓen Ɗan Majalisa na Ƙaura da aka yi baya cikin alƙawarin da aka yi mana, shugaban ƙasa ya yi mana alƙawalin zai duba lamarin tsaro na Jihar Zamfara, hakan ya sa ya ɗauki jihohi biyu da ya ci zaɓe, ya ba su ministocin tsaro, a Zamfara ba abin da aka yi mana.”

Kan kalaman da ake yi sun bar APC ne don ba a ba su muƙami ba ne? Ya ce haka ne, ai suna siyasa ne don su samu muƙami su amfanar da al’ummarsu, “don me wani zai tsaya takara mu yi kamfe a zaɓe shi a ƙarshe ya ce shi ba abin da zai ba mu, wannan ba adalci ba ne don haka mun jingine Jam’iyar APC.

“A nan gaba za mu sanar da jam’iyyar da muka koma, sai a yi yaƙin gaba da gaba kana can ina nan,” kalaman Kabiru Marafa.

Sakataren yaɗa labarai na Jami’iyar APC a Zamfara Yusuf Idris, ya ce ba za su ce komai ba kan kalaman Sanata Kabiru Marafa domin bai rubuta masu ya sanar da su ya bar APC ba tun daga kan mazaɓarsa har zuwa matakin jiha.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bello Matawalle Sanata Kabiru Marafa Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda